Hamɓarar da shugaba Ibrahim Boubacar Keïta ya haifar da fargaba kan makomar siyasar ƙasar Mali.
Ƙasashen duniya da dama sun yi allawadai da juyin mulkin, inda ake bayyana damuwa kan yiyuwar ƙazancewar rikici a Mali, wadda tuni ta ke fama da rikin mayaƙa masu da'awar jihadi da kuma rikicin ƙabilanci.
Sojojin da suka jagoranci juyin mulkin sun sanar da kafa kwamitin da zai tsara mayar da mulki ga farar hula sannan sun nuna cewa ba za su dawwama ba akan mulki.
Amma tambayar a nan ita ce, yaushe za a gudanar da zaɓe kuma wace rawa ƴan siyasa za su taka a wajen sauya gwamnatin?
Shugabannin ƙasashen Ecowas tuni suka mayar da hankali kan rikicin Mali inda suka fito da kuɗiri na kafa gwamnatin haɗaka domin magance rikicin siyasar ƙasar.
Ƴan adawa sun yi watsi da wannan buƙatar inda suka jaddada lalle zai shugaba Ibrahim Boubacar Keïta da Firaminista sun yi murabus.
Sojoji sun hamɓarar da shugaban ne ranar Talata inda suka yi amfani da buƙatar Ecowas na sanar da cewa za su kafa gwamnatin riƙon ƙwarya.
Ko wa zai jagoranci gwamnatin riƙon ƙwarya da sojoji ke magana? Soja ko kuma wani ɗan siyasa? ko wani daga ƙungiyoyin farar hula? Tambayoyi da babu amsarsu har yanzu.
Domin ƙarin bayani sai a karanta cikakken labarin a nan