Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Zan koma limanci tun da an kawar da Keita – Mahmoud Dicko

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai-tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai-tsaye, sai kuma gobe idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Ga wasu daga cikin labaran da muka wallafa a wannan shafin a yau:

    • ASUU za ta ci gaba da yajin aiki har sai an biya mata buƙatunta
    • Najeriya ta kashe kusan duka kuɗin shigarta na wata biyar a biyan bashi
    • Ganduje ya bai wa ma'aikatan Kano hutun sabuwar shekarar Musulunci
    • Kotun Ƙolin Indiya ta yi umarni a sake bincike kan mutuwar Sushant Rajput
    • Babban sifeton 'yan sanda ya bayar da umarnin sake kamo Sunday Shodipe
    • Za a buɗe wani kundi da za a rinƙa rajistar masu fyaɗe a Ghana
    • Sama da 'yan ci-rani 40 suka mutu a hatsarin kwale-kwale a Libiya – MDD

    Za ku iya duba ƙasa domin karanta waɗannan labaran da ma wasu muhimmai.

  2. Darajar kamfanin Apple ta kai dala tiriliyan biyu a kasuwar hannayen jari

    Kamfanin Apple ya zama kamfani mai zaman kansa na farko da darajar hannayen jarinsa ta kai dala tiriliyan biyu a kasuwar hada-hadar zuba hannayen jari ta Wall street.

    Farashin jarinsa ya ninka tun bayan da ya fuskanci faɗuwa a watan Maris ɗin da ya gabata sakamakon annobar korona wanda hakan ya tilasta wa kamfanin rufe wasu kantunansa.

    Sai dai tun bayan wannan lokacin ne kamfanin ya samu ƙaruwa a kuɗaɗen shigarsa, saboda ƙaruwar da aka samu a yawan ma'aikata da ke aiki daga gida a sasan duniya daban daban.

    Manyan kamfanonin ƙere-ƙere na kayayyakin kimiyya sun samu riba matuƙa a watannin da suka wuce idan aka kwatanta da sauran kasuwanci.

    Kamfanin mai na Saudi Aramco, wanda mallakar ƙasar Saudiyya ne, shi ne ya taɓa zama na farko da aka ƙimanta darajarsa kan dala tiriliyan biyu lokacin da ya fara sayar da hannun jarinsa a bara, sai dai tuni kamfanin ya yi warwas.

  3. Juyin mulki a Mali: 'Zan koma limanci tun da an kawar da Keita'

    Ɗaya daga cikin jagoran 'yan adawa a Mali ya ce zai koma masallaci domin ci gaba da limanci tun da burinsa ya cika.

    Imam Mahmoud Dicko na daga cikin manyan da suka rinƙa jagorantar zanga-zanga a Mali da ta yi sanadiyyar hamɓarar da gwamnatin Shugaba Keita.

    A daren jiya ne dai za a iya cewa burinsu ya cika, bayan wasu 'yan tawaye daga sojojin ƙasar suka kama shugaban.

    Imam Dicko ya kasance kan gaba wurin zanga-zanga, inda ya rinƙa jagorantar sama da mutum dubu goma a titunan Bamako babban birnin ƙasar.

  4. Abin al'ajabi: Ruwa ya bar gangare yana haurawa tudu

  5. 'A yi bincike kan mutum huɗu da aka kashe a Mali ranar Talata'

    Ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Amnesty International ta buƙaci sojojin Mali da su gudanar da bincike kan wasu mutum huɗu da aka kashe, da kuma wasu 15 da aka yi wa rauni a ranar Talata da aka yi juyin mulki a ƙasar.

    A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta kuma buƙaci sojojin ƙasar su daina kama mutane ba gaira ba dalili suna tsare su.

    Biyo bayan juyin mulkin da aka yi a ƙasar ta Mali, sojojin ƙasar sun kutsa gidan Shugaban ƙasar Ibrahim Boubacar Keita inda suka kama shi, tare da jami'an ƙasar da dama.

    Cikinsu har da ministan kuɗi na ƙasar Abdoulaye Daffé, da ministan harkokin wajen ƙasar Tiébilé Dramé da kuma ministan tsaro Janar Ibrahim Dahirou Dembelé.

  6. Labarai da dumi-dumi, Sama da 'yan ci-rani 40 suka mutu a hatsarin kwale-kwale a Libiya – MDD

    Akalla 'yan ci-rani 45 ne, ciki har da yara biyar suka mutu a wani hatsarin kwale-kwale mafi muni da ya faru a wannan shekarar a gaɓar tekun Libiya, in ji Hukumar Majalisar Ɗinkin Duniya da ke kula da 'yan ci-rani.

    Suna cikin mutum 80 da ke cikin wani kwale-kwale da injin ɗinsa ya yi bindiga a gaɓar tekun Zwara, in ji hukumar.

    Wasu mutum 37 da suka tsira ne suka bayar da rahoton haka. Su ma waɗanda suka tsira ɗin wasu masu sana'ar kamun kifi suka ceto su.

    Hukumar Majalisar Ɗinkin Duniya da ke kula da 'yan ci-rani da kuma ƙungiyar kula da 'yan ci rani ta duniya sun yi kira da a matsa ƙaimi wurin ceto waɗanda hatsarin ya rutsa da su.

    Sun bayyana cewa idan ba a dage wurin neman waɗanda suka yi hatsarin ba, za a ƙara asarar wasu rayukan a tekun Mediterranean.

    Waɗanda suka tsira yawancinsu 'yan Senegal ne, da Mali da Chadi da Ghana.

  7. 'Yan Najeriya da ke kasuwanci a Ghana sun gudanar da zanga-zanga

    ‘Yan Najeriya da ke gudanar da kasuwanci a ƙasar Ghana sun yi zanga-zangar lumana a gaban ofishin harkokin ƙasashen wajen ƙasar a Abuja.

    Masu zanga-zangar, waɗanda ke ɗauke da kwalaye ɗauke da rubutu iri daban-daban na nuna fushinsu kan yadda hukumomin Ghana ke ci gaba da rufe musu shaguna sun bayyana cewa lokaci yayi da gwamnatin kasar ya kamata ta dauki mataki.

    Masu zanga-zangar dai sun ce abin da ake yi musu a Ghana ya isa haka, don haka ya kamata gwamnati ta ɗauki mataki.

    Ko a mnakon da ya gabata sai da aka rufe sama da shaguna 40 na baƙi sakamakon gudanar da kasuwanci ba bisa ƙa'ida ba.

    Dokar ƙasar dai ta haramta wa baƙi waɗanda ba 'yan ƙasar ba buɗe shaguna domin goggaya da 'yan ƙasar wurin sayar da kayayyaki, amma kuma ba a haramta wa baƙn dillancin kaya ba.

    Ko a shekarar da ta gabata sai da wasu mutane daga ƙungiyar 'yan kasuwa ta Ghana suka kulle shagunan baƙi mazauna ƙasar, kuma akasari shagunan mallakar 'yan Najeriya ne da 'yan China.

  8. Taiwan na zargin China da yi mata kutse

    Taiwan ta bayyana cewa wasu gungun masu kutse a shafukan intanet da ke da alaƙa da gwamnatin China sun yi kutse ga akalla shafuka 10 na hukumomi a Taiwan.

    Taiwan ɗin ta bayyana cewa an yi mata kutsen ne da yunƙurin satar mata bayanai.

    Wani jami'i da ke sa ido kan kutsen intanet a Taiwan Liu Chia-zung, ya bayyana cewa an yi kutse ga wurin ajiye saƙonni na E-mail kusan dubu shida a shekaru biyu da suka gabata, kuma har yanzu ba a gama gano irin ɓarnar da aka yi ba.

    Jami'ai a ƙasar sun ce akalla wasu ƙungiyoyi sanannu da suka shahara wurin kutse a China, wato Blacktech da Taidoor na cikin waɗanda ake zargi.

    Akwai kuma wasu kamfanonin Taiwan huɗu da ke samar wa gwamnatin sabis na intanet da aka yi wa kutsen.

    Ana dai samun zaman ɗar-ɗar tsakanin China da Taiwan, wadda Beijing ɗin ke kiranta a matsayin yankinta.

  9. Ina Mali ta tafka kuskure?

      • Marubuci, Andrew Harding
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC News, Johannesburg

    Yaƙin da aka yi a Libiya fiye da shekaru 10 ne ya sa ƙasar a hanyar rikicin da take ciki.

    Makaman da aka yi amfani da su a Libiya sun ta yawo a cikin Sahara, wanda hakan ya rura wutar rikicin 'yan aware a arewacin Mali, wanda rikicin daga baya ya koma na masu iƙirarin jihadi, hakan ya jawo juyin mulki a halin yanzu a ƙasar.

    A yanzu, dakarun Faransa, da jirage mara matuƙa na Amurka da sojojin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya da kuma jirage masu saukar ungulu na Birtaniya na ƙoƙari da kuma gazawa wurin tabbatar da tsaro ba wai a Mali kawai ba, amma a faɗin yankin wanda a kullum yana ƙara samun barazana ta masu iƙirarin jihadi da kuma wasu rikice-rikice.

    Juyin mulkin baya-bayan nan da aka yi a Bamako tamkar manuniya ce kan matsalar tsaro da cin hanci da rashawa da rikicin zaɓe da rikicin siyasa.

    Da alamu shi kansa juyin mulkin ba zai sauya komai ba.

    Amma hakan na nuna amfaninsa – sa bakin da ƙasashe ke yi na da amfani, mabuɗin gyara ƙasa kamar Mali yana hannun ƙasar, da kuma 'yan siyasar ƙasar.

  10. Za a buɗe wani kundi da za a rinƙa rajistar masu fyaɗe a Ghana

    Hukumomi a Ghana na ƙoƙarin buɗe wani kundi da za a rinƙa yin rajistar sunayen waɗanda aka samu da laifin fyaɗe ko kuma ayyuka makamantan haka.

    Wani bincike da BBC ta gudanar a wasu jami'o'i ciki har da wata jami'a a Ghana kan yadda wasu malamai ke cin zarafin ɗalibai ta hanyar lalata na ɗaya daga cikin dalilan da suka sa aka sake bayar da muhimmanci kan batun fyaɗe a ƙasar.

    'Yan sandan ƙasar ta Ghana sun ce wannan rajistar da za a buɗe ba wai za ta taimaka wurin yaƙi da masu fyaɗe ba kaɗai, za ta zama darasi ga waɗanda ke da niyyar aikata irin laifin.

  11. Babban sifeton 'yan sanda ya bayar da umarnin sake kamo Sunday Shodipe

    Babban Sifeton 'Yan sandan Najeriya Mohammed Adamu, ya tura ƙarin jami'ai masu bincike zuwa jihar Oyo, domin taya rundunar 'yan sandan jihar gudanar da bincike kan tserewar da Sunday Shodipe ya yi daga hannun 'yan sanda.

    Mista Sunday Shodipe ya tsere daga wurin 'yan sanda ne bayan kama shi bisa zarginsa da kisa.

    A wata sanarwa da rundunar 'yan sandan ƙasar ta fitar, ta ce jami'an da aka tura za su yi amfani da ƙwarewarsu ta aiki wurin taimakawa domin sake kama wanda ake zargin.

    'Yan sandan na zargin Mista Sunday da aiwatar da kisa daban-daban a Ƙaramar Hukumar Akinyele a jihar Oyo.

    Babban sifeton ya nuna rashin jin daɗinsa kan guduwar da Mista Sunday ya yi a hannun 'yan sanda, ya kuma bayar da umarnin sauya fasalin rundunar 'yan sandan a jihar ta Ooyo domin gudun sake afkuwar irin wannan lamarin.

  12. Kotun Ƙolin Indiya ta yi umarni a sake bincike kan mutuwar Sushant Rajput

    Kotun ƙoli a Indiya ta umarci hukumar bincike ta ƙasar kan ta duba batun mutuwar fitaccen jarumin Bollywood ɗin nan watau Sushant Singh Rajput.

    A watan Yunin da ya gabata ne aka gano gawarsa a gidansa da ke Mumbai, imnda 'yan sanda suka ce ya kashe kansa.

    Mutuwar tasa ta janyo ce-ce-ku-ce tsakanin magoya bayansa da kuma wasu abokan aikinsa.

    An saka siyasa tare da nuna damuwa a binciken farko da 'yan sanda suka yi, wanda ya shafi iyalin mamacin da budurwarsa da 'yan sanda da kuma 'yan siyasa a wasu jihohi biyu na ƙasar.

    Wakiliyar BBC ta ce mahaifin tauraron ya shigar da ƙara gaban kotu yana zargin buduwar marigayin mai suna Rhea Chakarabothy da sa ɗansa cikin damuwa.

    Kazalika, ya zarge ta da cewa ba ta yi masa adalci ba a harkar da ta shafi kuɗi. Sai dai Kotun Ƙolin ta ce bincike mai zaman kansa ne zai tabbatar ko an yi adalci ga wadanda ba su aikata laifi ba.

  13. Miliyoyin mutane za su shiga wani hali a Yemen – MDD

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin miliyoyin mutane a Yemen za su wahala kuma wataƙila su rasa rayukansu saboda rashin tallafin gudanar da ayyukanta na jin kai.

    Lise Grande, wadda babbar jami'a ce a MDDR, ta ce an rufe kusan kashi ɗaya bisa uku na manyan shirye-shiryen bada agaji ko kuma an matuƙar rage yawan ayyukan bada agaji, haka kuma an rage yawan abinci da ake bai wa mutane fiye da miliyan takwas .

    Madam Grande ta ce muddin ba a samar da ƙarin tallafi a cikin makonni masu zuwa ba, toh za a dakatar da kayayyakin da ake kai wa asibitoci da dama.

  14. Ganduje ya bai wa ma'aikatan Kano hutun sabuwar shekarar Musulunci

    Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana gobe Alhamis a matsayin ranar hutun ma'aikata a jihar albarkacin ranar ɗaya ga watan sabuwar shekarar Musulunci ta 1442.

    A jiya Talata ne Fadar Sarkin Musulmi a Najeriya ta fitar da sanarwa tana umartar al'ummar Musulmi da su fara duba sabon watan Muharram a daren yau Laraba, wanda shi ne watan farko a kalandar Musulunci.

    Cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na intanet, Fadar Gwamnatin Kano ta ce Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya shawarci mazauna jihar da su yi amfani da hutun domin yi wa Kano addu'o'in zaman lafiya da ci gaba.

    Kazalika gwamnan ya buƙaci mutane "su ji tsoron Allah a harkokinsu na yau da kullum domin samun sauƙi game da wahalhalun tattalin arziki da ake ciki" sannan kuma su zauna lafiya da juna.

    Bisa tsarin kalandar Musulunci, idan an ga watan a daren Laraba to Alhamis ce ranar ɗaya ga sabuwar shekarar. Idan ba a gani ba kuma, za a cika watan Zul Hijja kwana 30 - watan ƙarshe - sai Juma'a ta zama ranar sabuwar shekara.

  15. Boko Haram ta kai hari a Borno

    Rahotanni daga Jihar Borno da ke arewaci maso gabashin Najeriya na cewa ƙungiyar ƙungiyar Boko Haram ta kai hari garin Kukawa da ke kusa da Tafkin Chadi sannan suka hana mazauna garin tserewa.

    Ya zuwa yanzu hedikwatar tsaron ƙasar ba ta ce komai ba game da harin.

    Abu ne mai wuya a iya tabbatar da haƙiƙanin abin da ya faru sakamakon katse layukan wayar salula a yankin.

    Za mu kawo muku ƙarin bayani da zarar mun samu.

  16. Najeriya ta kashe kusan duka kuɗin shigarta na wata biyar a biyan bashi

    Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta kashe kashi 97.5 cikin 100 na kudin shigarta na Janairu zuwa Mayu a kan biyan bashi.

    Bisa tsarin kasafin kudin shekarar 2021 da ofishin kasafin kudi ya fitar, Gwamnatin Tarayya ta samu jumillar kudaden shiga naira tiriliyan N1.62 maimakon tiriliyan N2.62 da ya kamata ta samu a wannan lokacin.

    A cikin wata biyar din, an biya bashin tiriliyan N1.58; kashi 97.5 kenan cikin 100 na tiriliyan N1.62 da aka samu na kudin shiga.

    A watan Yuni, asusun bayar da lamuni na duniya IMF ya yi hasashen cewa biyan bashi zai lamushe baki dayan kudin shigar Gwamnatin Tarayyar Najeriya.

    A cewar wasu bayanai da aka wallafa, Gwamnatin Tarayyar ta kashe tiriliyan N3.98 a cikin wata biyar; an ware tiriliyan N1.79 kan ayyukan yau da kullum da babu biyan bashi a cikinsu, waɗanda suka haɗa da albashi da fansho.

  17. 'Abin da ke faruwa ga 'yan Najeriya a Ghana ya saɓa wa dokokin ECOWAS'

    Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Femi Gbajabiamila ya ce abin da hukumomin ƙasar Ghana ke yi na rufe shagunan 'yan kasuwar Najeriya "ya saɓa wa dokokin ƙungiyar Ecowas ta raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma.

    Femi ya ce sun tattauna da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Geoffrey Onyeama da kuma Niyi Otumba Adebayo, tsohon gwamnan Jihar Ekiti game da batun.

    A jiya ne Ma'aikatar Harkoikin Wajen Najeriya ta tabbatar wa da BBC cewa sun gayyaci jadakan Ghana a Najeriya domin bayyana rashin daɗinsu game da halin da 'yan kasuwar Najeriyar ke ciki a ƙasar.

    "Abin da ke faruwa a Ghana lallai ya saɓa wa ƙa'idojin ƙungiyar ECOWAS kuma wajibi ne a magance shi domin ci gaban ƙasashen biyu," in kakakin, a wani saƙo da ya wallafa yau Laraba a Twitter.

    The happenings in Ghana are indeed against the spirit of the ECOWAS protocol and must be dealt with decisively in the interest of both countries.

    Tun a makon da ya gabata ne hukumomi a Ghana suka fara rufe shagunan ƙananan 'yan kasuwar na ƙasashen waje da ke birnin Accra - mafi yawansu 'yan Najeriya - bisa abin da suka kira rashin mallakar takardu.

  18. Barcelona ta naɗa Ronald Koeman a matsayin kocinta

    An naɗa Ronald Koeman a matsayin sabon kocin Barcelona kwana biyu bayan koran Quique Setien.

    Ɗan shekara 57 din ya ajiye aikin horar da tawagar ƙasar Netherlands da saura shekara biyu a kwangilarsa domin ya sanya hannu a kwangilar shekara biyu da Barcelona.

    Ya buga wa Barcelona tamaula a tsakanin shekarun 1989 zuwa 1995 har ma ya taimaka musu lashe kofin La Liga huɗu da kofin Zakarun Turai na Champions League ɗaya.

    Barcelona ta kammala kakar wasa ta bana a mataki na biyu a La liga, inda ta kasa cin kofi ko ɗaya a karon farko tun kakar 2007-2008.

    Ratar maki biyar da Real Madrid ta ba ta da ƙwallo takwas da kuma ragargazar da Bayern Munich ta yi mata a Champions League makon da ya wuce ne suka sa aka kori Setiein ranar Litinin.

    Kungiyar ta naɗa Ramon Planes a matsayin daraktan tsare-tsare. Shi ne mataimakin Eric Abidal, da ya sauka daga kujerar daraktan wasanni ranar Talata.

    Koeman zai yi jawabi a taron manema labarai da karfe 5:00 agogon Najeriya da Nijar.

  19. Kamaru: Ana shirya fim kan halin da mutane ke ciki a yankin rainon Ingila

    Wata ƙungiya mai zaman kanta da ake kira ADISI ta fitar da wani bidiyo na musamman mai kunshe da irin halin da mutane ke rayuwa a yankin rainon ingila na ƙasar Ingila.

    Yankin na rainon Ingila ya dade yana fama da rikicin masu fafutuka da ke yunkurin kafa kasar Ambazoniya.

    Kungiyar wadda take mayar da hankali wurin bincikar wani lamari mai sarkakiya da yada akidar ‘yancin ‘yan jaridu, ta kwashe wata huɗu tana haɗa abin da za a iya kira fim na musamman.

    Fim zai nuna matasa wadanda ka iya rasa mafita a rayuwarsu duk da irin kokarin da masu aikin agaji ke yi a yankin nasu.

  20. Shugabannin Afirka ta Yamma za su je Mali a yau

    Anjima a yau Laraba ake sa ran tawagar wakilai ta shugabannin ƙasashen yammacin Afirka za su isa ƙasar Mali, a cewar shafin Studio Tamani na ƙungiyar haɗin kan Afirka ta AU.

    Shugabannin ƙasashen Nijar da Senegal da Ghana da Ivory Coast ne ake sa ran za su yi wakilcin.

    A baya, shugabannin ƙasashen ƙungiyar Ecowas sun yi yuynƙurin sasanta rikici a lokuta daban-daban ciki har da yunƙurin kafa gwamnatin haɗaka.

    Sai dai 'yan adawa sun yi watsi da yunƙurin kuma suka haƙiƙance cewa sai Shugaba Ibrahim Boubacar Keïta ya sauka daga mulki.

    Da yammacin Talata ne sojoji suka tilasta wa Keita sauka daga muƙamin nasa sannan suka hau karagar mulki tare da yin alƙawarin shirya sabon zaɓe.