Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Najeriya ta sanar da ranar dawo da jigilar jiragen ƙasashen waje

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai-tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail, Halima Umar Saleh and Awwal Ahmad Janyau

  1. An kama sanatocin Kenya game da raba kudi ga yankunan ƙasar

    Sanatocin Kenya sun ce an kama abokan aikinsu uku a daren Lahadi game da zaɓen raba kudade ga ƙananan hukumomi.

    Kaɗa ƙuri'a a kan raba kudade da za a yi ranar Litinin, an daga shi sau takwas yanzu game da rashin jituwa a kan tsarin raba biliyan 316.5 na kuɗin Kenya (dalar Amurka biliyan $2.9) a tsakanin ƙananan hukumomi 47.

    Tsohon shugaban masu riinjaye Kipchumba Murkomen ya faɗa wa Majalisar Dattijai cewa an kama Cleophas Malala da Christopher Langat a gidajensu a babban birnin Nairobi, shi kuma Ltumbesi Lelegwe an kama shi a kan hanyarsa yta zuwa majalisar.

    Har yanzu 'yan sanda ba su ce komai ba kan batun ba.

    Sanatocin sun kira da a sake gabatar da ƙara don yin mahawara game da kama abokan aikinsu.

  2. Labarai da dumi-dumi, Kotu ta soke zaɓen Gwamna Diri na Jihar Bayelsa

    Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Jihar Bayelsa ta soke zaɓen Gwamna Duoye Diri.

    Jaridar Premium Times ta rawaito cewa an soke zaɓen ne sakamakon ƙorafin da jam'iyyar Advanced Nigeria Democratic Party (ANDP) ta gabatar, inda ta ce an cire ta daga takardar kaɗa ƙuri'a ba bisa ƙa'ida ba.

    Sai dai za a iya ɗaukaka ƙara game da hukuncin a Kotun Ɗaukaka Ƙara.

    Hukuncin na ranar Litinin na zuwa ne kwana biyu bayan kotun ta kori wasu ƙorafi uku game da zaɓen Gwamna Diri na jam'iyyar PDP.

    Nan gaba za a bayar da cikakkun bayanai game da dalilan da kotun ta dogara da su na soke zaɓen.

  3. Ɗaruruwan 'yan zanga-zanga na nuna rashin amincewa da takunkumin korona a Spaniya

    Masu zanga-zanga sun taru a babban birnin Spaniya ranar Lahadi domin bayyana rashin amincewarsu da tilasta amfani da takunkumi rufe fuska da sauran matakan da a ka sanya na hana yaɗuwar annobar korona.

    An fara zanga-zangar kwana biyu bayan gwamnatin ta gabatar da sabbin matakai, ciki har da hana shan taba a cikin jama’a.

    Kasar Spaniya ta fuskanci ƙaruwaa a adadin masu kamuwa da cutar tun da ta ɗage dokokin kulle na wata uku a karshen watan Yuni.

    Yawan waɗanda suka mutu a ƙasar ya wuce mutane 28,600.

  4. Ana ƙwalla rana mafi zafi da ba a taɓa irinta ba a duniya a Amurka

    Ana ƙwalla rana mafi zafi da ba a taɓa irinta ba a duniya a gandun daji na Death Valley a jihar California da ke Amurka a ma'aunin 54.4 na selshiyas.

    Hukumar Kula Da Yanayi ta Amurka ce ta tabbatar da hakan.

    Hakan na zuwa ne a yayin da ake tsananin zafi a gaɓar teku daga yammacin Amurka, inda ake hasashen ma'aunin zafin zai ƙaru a makon nan.

    Tsananin zafin ya jawo an ɗauke wutar lantarki a California har tsawon kwana biyu, bayan da cibiyar lantarkin ta daina aiki a ranar Asabar.

    Kafin yanzu, an taɓa samun tsananin zafi a digiri 54 ma'aunin salshiyas a yankin na Death Valley a shekarar 2013.

    A cewar wani sharhi da masanin tarihin yanayi Christopher Burt ya yi a 2016, sauran yanayin zafi da aka samu a yankin a shekarar 1913 bai yi daidai da na yankin Death Valley ba.

    Sannan ya ce a shekarar 1931 an samu wani zafin yanayin a digiri 55 na ma'aunin salshiyas a Tunusiya, sai dai ya ce an samu hakan ne a lokacin mulkin mallaka don haka babu sahihanci kan batun.

    A yayin da yanayin zafi ke ta'azzara a California, an yi guguwa mai ɗauke da wuta a ranar Asabar a yankin Lassen.

  5. Cutar korona ta kashe fiye da mutum 50,000 a Indiya

    Kididdigar hukumomi a Indiya ta nuna cewa yawan mutanen da cutar korona ta kashe a kasar ya haura dubu hamsin.

    Yanzu haka yawan wadanda cutar ta harba ya haura miliyan biyu da dubu dari shidda, abin da ya kara tabbatar da ita a matsayin kasa ta uku da cutar ta fi addaba a duniya.

    To sai dai hukumomin kasar na cewa duk da haka, adadin wadanda suka harbu da ya karu da akalla mutum miliyan guda a kwanaki 20 da suka gabata na sakkowa kasa sannu a hankali a yanzu.

    Wasu bayanai sun nuna cewa yawancin jihohin da ake samun karuwar wadanda ke kamuwa cikin hanzari kamar Bihar, da Uttar Pradesh da Orissa, ba sa iya kebe mutanen da suka je daga wuraren da cutar ke da tasiri.

  6. 'Buhari ba shi da alaƙa da gayyatar da DSS ta yi wa Ghali Na'Abba'

    Gwamnatin Najeriya ta nesanta kanta daga gayyatar da hukumar DSS ta yi wa Ghali Na'Abba bisa zargin yin kalamai kan Shugaba Muhammadu Buhari.

    Sanarwar da Garba Shehu - mai magana da yawun Fadar Shugaban Ƙasa - ya fitar ta ce bayanan da suka samu na farko-farko sun nuna cewa gayyatar da aka yi wa Ghali Na'Abba ba ta da alaƙa da maganganun da ya yi.

    A yau Litinin ne ake sa ran tsohon Kakakin Majalisar Wakilan na Najeriya zai amsa gayyatar da DSS ta yi masa bayan wasu kalaman neman kawo sauyi a Najeriya da ya yi a makon da ya gabata.

    Ya yi kalaman ne ƙarƙashin wata ƙungiya mai suna National Consultative Front.

    "Buhari na sane da alfanun samun ƙwaƙkwarar jam'iyyar adawa ganin cewa shi ma daga nan ya fito," a cewar sanarwar.

    "Shugaban ƙasa ya faɗin cewa burinsa shi ne ya gudanar da zaɓe mai inganci da zai bai wa 'yan ƙasa damar ɗora wanda suke so a kan mulki kuma duk wani abu akasin haka ba abin so ba ne."

  7. Gwamnatin Najeriya za ta ɗauki mataki kan rufe shagunan 'yan ƙasar a Ghana

    Gwamantin Najeriya ta bayyana ta ce za ta ɗauki "matakin gaggawa" game da wani bidiyo da ya ɓulla a shafukan sada zumunta da aka ce 'yan Najeriya ne ake wulaƙantawa a Ghana.

    Bidiyon ya nuna jami'an tsaro suna garƙame shagunan 'yan kasuwar ƙasashen waje da ƙarfin tsiya, waɗada akasarinsu 'yan Najeriya ne.

    Ministan harkokin wajen Najeriya, Geoffrey Onyeama ne ya bayyana hakan, yana mai cewa ba su ji daɗin abin da suka gani ba.

    "Gwamnatin Najeriya ba ta ji daɗi ba game da bidiyon da ya nuna yadda ake rufe shagunan 'yan Najeriya a Ghana da ƙarfin tsiya. Za mu ɗauki matakan gaggawa," in ji Onyeama.

    Gwamnatin Ghana ta jaddada cewa za ta ci gaba da rufe shagunan ƙananan 'yan kasuwar waɗanda mafi yawansu 'yan Najeriya, har sai sun mallaki takardun da suka dace.

  8. An kawo ƙarshen harin al-Shabab a Somaliya

    Dakarun musamman a Somalia sun kawo ƙarshen garkuwa da 'yan ƙungiyar al-Shabab suka yi da wani otel ranar Lahadi.

    Aƙalla mutum 11 ne suka mutu a otal ɗin Elite haɗi da 'yan bindiga guda biyar, a cewar wata sanarwa daga mai magana da yawun gwamnati.

    Maharan sun dasa bam a cikin wata mota a wajen otal ɗin kafin daga baya su shiga tare da yin garkuwa da mutanen ciki.

    Otal ɗin da aka gina kwanan nan, mallakar wani ɗan majalisa ne da ke da alaƙa da jami'an gwamnati.

    Sahidun gani da ido sun ce an ji ƙarar fashewar a ɗaukacin birnin Mogadishu, inda aka samu yamutsi yayin da mutane suke ƙoƙarin barin wurin da abin ya faru.

  9. Ana shirin buɗe zirga-zirgar ƙasa da ƙasa a Ghana

    Shugaban Ghana Nana Akufo-Addo ya ce yana shirin sahale zirga-zirgar jiragen sama daga ƙasashen waje zuwa ƙasarsa daga ranar 1 ga watan Satumba.

    An dakatar da jirage shiga da fita daga ƙasar tun a watan Maris sakamakon annobar korona. Adadin waɗanda ke kamuwa da cutar a kullum yajna raguwa a 'yan kwanakin nan.

    Da ma tuni jirage masu zirga-zirgar cikin gida suka ci gaba da harkokinsu a Ghana.

    Kazalika, shugaban ya sanar da buɗe makarantun gaba da sakandare a mako mai zuwa tare da sassauta dokokin kulle na yaƙi da cutar.

  10. Barkanku da shigowa shafin labarai kai-tsaye

    Wannan shafi zai ria kawo muku labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a sassan duniya musamman Najeriya da mawabtanta a wannan rana ta Litinin - tushen aiki ko nasara na tsoronki.

    Umar Mikail ke cewa ku biyo mu.