Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Tawagar da Buhari ya aika ta'aziyyar rasuwar Inyass ta isa Senegal

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Buhari Muhammad Fagge and Mustapha Musa Kaita

  1. Cutar korona ta kashe mutum fiye da dubu 50 a Mexico

    Hukumomin lafiya a Mexico sun ce yawan mutanen da suka mutu sanadin annobar korona ya karu zuwa fiye da dubu 50.

    Amurka da Brazil ne kadai kasashen da suka fi yawan wadanda wannan cuta ta shafa.

    A farkon makon nan ne Shugaba Andres Manuel Lopez ya sanar cewa zai rika yin shiru na minti daya duk rana domin tunawa da wadanda suka mutu.

  2. Trump zai kori TikTok da Wechat daga Amurka

    Shugaba Trump ya rattaba hannu kan wata dokar shugaban kasa wacce za ta haramta duk wata harkar kasuwanci da Amurka za ta yi da uwar kamfanin wasu kamfanonin China biyu na fasahar sadarwa.

    Takunkumin kan kamfanin ByteDance, wanda ya mallaki manhajar TikTok, da Tencent, da kuma uwar kamfanin sadarwa na Wechat zai fara aiki ne nan da kwana arba'in da biyar.

    Shugaban ya ce dole ne ya sa ya dauki tsatssauran mataki domin kare tsaron kasarsa.

    Dokar ta shugaban kasar ta bayyana cewa Tiktok da Wechat suna barazana ga tattalin arziki da kuma tsaron Amurka.

    Kamfanin Microsoft ya nuna sha'awar sayen TikTok, sai dai wannan dokar ta shugaban kasar ta toshe yiwuwar kammala wannan yarjejeniya.

  3. Covid-19: Za a yi Sallolin Juma'a karon farko cikin wata hudu a Lagos

    Musulmi a Lagos, babban birnin kasuwancin Najeriya, za su gudanar da sallolin Juma'a karon farko cikin watan hudu.

    Kazalika ranar Lahadi za a gudanar da ibadu a coci-cci.

    An rufe masallatai da coci-coci a watan Maris sakamakon annobar korona.

    Gwamnan jihar Lagos Babajide Sanwo-Olu ya ce za a sake bude wuraren ibada ne sakamakon ci gaban da ake samu a yakin da jihar ke yi da cutar korona.

    Sai dai za a bar wuraren ibadar ne kawai su kyale kashi 50 na mutanen da suka kamata su gudanar da ibada su shiga cikinsu.

    Gwamnati ta ce dole ne masu ibada su dauki matakan kariya kamarsu sanya takunkumi da nesa-nesa da juna.

  4. Budewa

    Buhari Muhammad ne yake yi muku barka da warhaka.

    Muna fatan za ku kasance tare da mu tsawon wannan rana domin sanin halin da duniya take ciki.

    Za mu kawo muku labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku, musamman kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da makwabtansu, har ma da sassan duniya.

    Kuna iya bibiyarmu a shafukan sada zumunta don tafka muhawara da bayyana ra'ayoyinku.