Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Tawagar da Buhari ya aika ta'aziyyar rasuwar Inyass ta isa Senegal

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Buhari Muhammad Fagge and Mustapha Musa Kaita

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye, sai kuma gobe Asabar idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Ga wasu daga cikin labaran da muka wallafa a wannan shafin.

    • An kashe mutum 21 a kudancin Kaduna
    • Naira Marley ya amsa laifin saɓa dokar kulle
    • INEC ta samar da shafin da za a rika bibiyar zaɓe kai tsaye
    • Sallar Juma'a karon farko a Legas bayan sama da watanni huɗu
    • Adadin waɗanda suka mutu a Beirut ya kai 154
    • Buhari ya amince da Ize-Iyamu a matsayin ɗan takarar APC a Edo
    • Ƙungiyar Shi'a ta Hezbollah ta nisanta kanta da fashewar sinadarai a Lebanon

    Za ku iya duba ƙasa domin karanta waɗannan labaran da ma wasu muhimmai

  2. Kanada za ta zabga wa Amurka haraji kan sanholo

    Kasar Kanada za ta mai da raddi ga Amurka, ta hanyar sanya wani haraji na kimanin dala biliyan biyu da miliyan dari bakwai a kan ma`adinin sanholo ko kuma aluminium a turance, na Amurka da ake shiga da shi Kanada, bayan Shugaba Trump ya sanar da ƙarin kashi goma cikin ɗari na irin wannan harajin a kan goran-ruwan Kanada da ake shigarwa Amurka.

    Mataimakiyar Firaministan Kanada, Chrystia Freeland ta bayyana matakin da Trump ɗin ya ɗauka da cewa ya saɓa wa hankali, tana cewa saɓani a harkar kasuwanci a wannan lokaci da ake fama da annobar korona ba abin so ba ne, sai ta baci.

    Ta kara da cewa harajin zai fara aiki ne daga ranar 16 ga watan Satumba, domin a samu lokacin tantance irin kayan da za a yi wa harajin.

    Shugaba Trump ya zargi kasar Kanada da cika kasuwannin Amurka da Sanholo, kuma a ranar 16 ga wannan watan na Agusta ne Amurka za ta fara karbar harajin.

  3. Tawagar da Buhari ya aika ta'aziyyar rasuwar Inyass ta isa Senegal

    Tawagar Gwamnatin Najeriya ƙarkashin jagorancin Shugaban kamfanin NNPC Mele Kyari ta isa Senegal domin ta'aziyyar rasuwar jagoran Ɗariƙar Tijjaniya a Afrika wato Sheik Khalifa Ahmed Tijjani Inyass.

    A wani saƙo da mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan kafofin watsa labarai na zamani Bashir Ahmed ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya bayyana cewa cikin waɗanda suka je ƙasar yin ta'aziyyar amadadin Shugaba Buhari, akwai Shugaban hukumar kula da shige da fice ta Najeriya Muhammed Babandede.

    A wannan makon ne dai Marigayi Sheik Khalifa Ahmed Tijjani Inyass ya rasu, kuma tuni aka yi jana'izarsa a birnin Kaulaha da ke ƙasar

  4. An fitar da mutum biyar daga jirgi saboda zargin korona

    Hukumomin lafiya a Liberia sun bayyana cewa sun yi amfani da ƙarfin tuwo wurin killace wasu mutum biyar da aka fitar da su daga cikin jirgi yayin da suka yi yunƙurin komawa Amurka bayan sun halarci wata jana'iza.

    Lamarin ya faru ne yayin da aka samu labarin cewa ɗaya daga cikin waɗanda suka yi tafiya da mutanen ya mutu a Monrovia, kuma ana zargin korona ce ta kashe shi.

    Ɗaya daga cikin waɗanda aka killace ƙarfi da yaji ya shaida wa BBC cewa dukansu 'yan asalin ƙasar Liberia ne.

    Ya bayyana cewa sakamakon gwajin da aka yi musu ya nuna cewa ba su ɗauke da cutar, kuma akwai damuwa ganin cewa idan suka ci gaba da zama a Liberia za su iya rasa aikinsu a Amurka.

  5. Labarai Cikin Minti Ɗaya

    Latsa alamar lasifikar da ke sama domin sauraron labaran.

  6. Ƙungiyar Shi'a ta Hezbollah ta nisanta kanta da fashewar sinadarai a Lebanon

    Shugaban ƙungiyar Hezbollah, Hassan Nasrallah, ya musanta zargin da ake yi kan cewa fashewar sinadaren da aka samu a Beirut babban birnin Lebanon na da alaƙa da ƙunigyarsa ta Shi'a mai ƙarfi a ƙasar.

    A jawabinsa na farko tun bayan ƙazamin lamarin da ya faru a ƙasar, Nasrallah ya yi watsi da zargin da ake yi cewa Hezbollah ce ke da iko da tashar jirgin ruwan da fashewar abubuwan ya faru.

    Ya kuma bayyana cewa ƙungiyarsa ba ta yi ajiyar komai a wurin ba - walau harsasai ko bama-bamai ko kuma sindarin nitrates.

    Ya ce waɗanda ke alaƙanta ƙunigyar Hezbollah da wannan lamari na neman a yi yaƙin basasa ne kawai.

    Jawabin nasa na zuwa ne sa'o'i kaɗan bayan Shugaban Lebanon Michel Aoun ya yi watsi da binciken da ake son yi na ƙasa da ƙasa kan lamarin, inda ya ce akwai yiwuwar sa hannun wasu ƙasashe kan wannan lamari.

  7. 'Maleriya za ta iya kashe mutum 779,000 saboda karancin gidan sauro'

    Bincike ya nuna cewa rarraba gidan sauro a nahiyar Afrika zai iya rage mace-macen da cutar Maleriya ke haddasawa da kusan kashi 50 cikin 100.

    Akwai damuwa kan cewa annobar korona ta kawo cikas ga rabon da aka saba yi na gidan sauro a nahiyar.

    Ya kamata a ce an rarraba gidan sauro kusan miliyan 228 a ƙasashen Afrika.

    Sai dai wata makaranta a Birtaniya wato Imperial College ta yi hasashen cewa mutanen da Maleriya za ta kashe a wannan shekarar zai ninka sau biyu kan yadda aka saba samu a baya muddin aka samu tsaiko wurin ɗaukar matakan kariya.

    Binciken ya nuna cewa akwai yiwuwar cewa kusan mutum 779,000 cutar Maleriya za ta kashe cikin shekara guda .

  8. Buhari ya amince da Ize-Iyamu a matsayin ɗan takarar APC a Edo

    Gwamnan jihar Yobe kuma Shugaban jam'iyyar APC na riƙo Mai Mala Buni ya shaida cewa Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya amince da Fasto Osagie Ize-Iyamu a matsayin ɗan takarar gwamna a jam'iyyar APC a jihar Edo.

    A wani hoto da mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan kafafen sada zumunta Bashir Ahmed ya wallafa a shafinsa na Twitter, an ga shugaban ƙasar yana miƙa wa Mista Iyamu tutar jam'iyyar APC.

    Ɗan takarar kuma ya yi watsi da zargin da ake yi cewa 'yan majalisar jihar 14 a ranar sun yi zama a gidansa domin tsige kakakin majalisar Edo domin zaɓen sabo.

    A kwanakin baya ne dai gwamnan jihar Edo Godwin Obaseki ya koma jam'iyyar PDP daga APC sa'annan kuma Osagie Ize-Iyamu ya koma APC daga PDP.

  9. Adadin waɗanda suka mutu a Beirut ya kai 154

    Adadin waɗanda suka mutu sakamakon fashewar sinadarai a Beirut babban birnin Lebanon ya kai 154.

    Kamfanin dillancin labarai na ƙasar ne ya ruwaito ministan lafiya na ƙasar inda ya ce akwai mutum 120 da suna cikin wani hali.

    Hamad Hassan ya bayyana cewa da dama daga cikinsu suna buƙatar tiyata ta gaggawa musamman wadanda gilas ya yanka su.

    Wannan lamarin na tashin hankali ya faru ne a Beirut babban birnin ƙasar wanda ya jikkata mutum sama da dubu biyar da kuma ɓarnar da ba a iya kiyastawa.

  10. Sallar Juma'a karon farko a Legas bayan sama da watanni huɗu

    An gudanar da Sallar Juma'a a masallatai daban-daban a birnin Legas da ke Kudancin Najeriya.

    An shafe sama da watanni hudu ba a gudanar da Sallar Juma'a a jihar ba sakamakon yunƙurin gwamnati na daƙile annobar korona ta hanyar hana taron jama'a.

    Jihar Legas ce dai a kan gaba a yawan masu korona a Najeriya inda kusan mutum 15,627 suka kamu da cutar a jihar.

  11. Masu makamai sun kai wa kungiyar likitocin Najeriya hari

    Wasu mutane dauke da makamai sun tarwatsa taron kungiyar likitocin Najeriya lokacin da suke kaɗa kuri'ar zaben jami'an kungiyar, an lalata akwatunan zaben da kuma kujerun jami'an zaben.

    Rahotanni daga kasar na cewa likitoci a jihar Enugu na cewa abokan hamayya ne a zaben suka biya mutanen domin wannan aiki.

    Rahotanin sun ce an ji wa likitoci da dama rauni yayin rikicin.

    Wani da ya shaida faruwar al'amarin ya ce mutanen da suka je wurin zaben sun kai 30 dauke da muggan makamai da suka rika harar likitocin da su.

    An kuma wallafa bidiyon yadda a bin ya faru a Twitter:

  12. Yadda China ke fitar da kaya waje ya karu a watan Yuni

    A wata alama kan cewa tattalin arzikin kasar China da na duniya na farfadowa, yawan kayan da China ke fitarwa zuwa kasashen ketare ya karu da kaso 7.2 cikin dari a watan Yuli, idan aka kwatanta da farkon wannan shekarar.

    Masana tattalin arziki da Reuters da Bloomberg suka yi magana da su sun yi hasashen raguwar fitar da kaya kasashen waje. Sai dai yadda China take siyan kaya zuwa kasarta ya ragu da kusan kashi 1.4 cikin 100 idan aka kwatanta da farkon wannan shekarar.

    A farkon watan Faburairu yadda China ke fitar da kaya ya ragu da kaso 20 - wanda wannan ce raguwa da aka samu cikin sauri a shekara uku.

    Amma tun byaan da aka janye dokar kulle aka kuma bude kamfanoni, yawan harkokin China ke karuwa.

  13. INEC ta samar da shafin da za a rika bibiyar zaɓe kai tsaye

    Hukumar zaben Najeriya INEC ta ce ta samar da wani shafin intanet da zai bai wa ‘yan kasar damar bibiyar kirga kuri’un zabe daga gida.

    Cikin wani sakon Twitter da ta wallafa a shafinta hukumar ta ce an samar da shafin ne domin karfafa gaskiya a harkokin zabe da dakile wuru-wuru da kuma tabbatar da an yi komi bude.

    INEC ta ce tana sane da cewa da yawa daga ‘yan kasar na da shakku kan yadda ake gudanar da harkokin zabe, kuma suna nuna wa a fili. Im da ta ce a wasu lokutan ma akan cin zabe da kuri’un da suka wuce wadanda aka kada yayin zaben.

    INEC ta ce ta samar da wannan shafi ne domin kawo karshen wannan abu.

    Sai dai hukumar ta ce babu tsarin yadda ake tattara sakamakon zabe a wannan ci gaba da aka samu, tattara sakamakon zabe zai ci gaba da kasancewa kamar yadda tsarin doka ya tanadar.

    Za a fara amfani da wannan ci gaba ne a zaben cike gurbi da za a yi a jihar Narasawa a ranar Asabar mai zuwa ta 8 ga watan Agustan 2020. Za a kara amfani da wananan shafi a zaben Jihar Edo da ke biya masa baya wanda zaa gudanar a watan satumba.

    Tuni dai wasu 'yan kasar suka fara bayyana ra'ayinsu kan wannan al'amari.

    Dorothy ta ce " wanene zai rika dora sakamakon ko wacce rumfar zabe a wannan shafi?

    Omo ya ce ku ,mayar mana da katin zaben mu na kai tsaye ku hada shi da lambobi irin na su NIN .. kun ga babu bukatar bin dogon layi na sa'o'i da yawa ... ku saukaka mana rayuwa.

  14. Paul Biya zai cika alkawari bayan shekaru 30

    Shugaban kasar Kamaru, Paul Biya zai cika alkawarin da ya dauka shekaru 30 da suka wuce ga tawagar ‘yan kwallon kasar da ta kai zagayen gab da na kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya a shekara 1990.

    A lokacin ya dauki alkawarin zai bai wa kowannensu gida kyauta saboda bajintar da suka yi.

    Sai dai uku daga cikin ‘yan tawagar Louis Paul Mfede, Benjamin Massing da kuma Stephen Tataw sun mutu.

    Kungiyar tsofaffin ‘yan kwallon Indomitable Lions ne ta rubuta wa shugaban kasar wasika domin ya cika alkwari.

    Gidajen da za a basu a Yaounde ne babban birnin kasar da kuma wasu a Douala da kuma birni Limbe

    Roger Milla, wanda shi ne mafi shekaru a cikin tawagar ya gode wa shugaban kasar saboda cika alkawarin.

  15. Gwamnonin Arewa sun yi tir da hare-haren kudancin Kaduna

    Kungiyar gwamnonin arewacin Najeriya ta yi alawadai da harin baya-bayan nan da aka kai Kudanci Kaduna wanda ya yi ajalin mutane 22 a ranar Laraba. Wanda har yanzu ba a kai ga kama ko daya daga cikin wadanda suka kai harin ba cikin kauyuka hudu na karamar hukumar Zangon Kataf da ke kudancin jihar.

    Cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar, shugaban kungiyar gwamnan jihar Plateau Simon Bako Lalong ya ce ci gaba da kai hare-haren da ake yi a kauyukan duk da cewa gwamnatin jihar Kaduna da sauran jami'an tsaro na iya kokarinsu na ganin sun kawo karshen ta shin hankalin da kowa ke ala wadai da shi na nuna har yanzu da sauran aiki a gaba.

    Wannan harin da aka kai na bayan nan da aka kai kauyen Atyab da ya shafi mutanen da babu ruwansu, ba kawai bakinciki da bacin rai ya haifar ba, har ma da kokarin mayar da hannun agogon baya da ya yi na gwamnatin jihar Kaduna na samar da zaman lafiya a jihar.

    Ya ce " Abin bakin ciki ne wannan kai hari kan mutanen da ba sa dauke da makamai domin ba su da mataimaki, abin alwadai ne da nadama.

    Muna kira ga jami'an tsaro su tashi tsaye wajen bankado wadannan masu laifi, kuma muna rokon jama'a da su taimaka wajen bayar da bayanan da za su kai ga kama wadannan mutane."

    Kungiyar ta jajantawa wadanda suka rasa 'yan uwansu da kuma gwamnan jihar Nasir el-Rufa'i, suna fatan ganin wannan rikici ya zo karshe.

  16. Naira Marley ya amsa laifin saɓa dokar kulle

    Mawaki dan Najeriya Azeez Fashola wanda aka fi sani da Naira Marley ya amsa laifin saba dokar kullen Covid 19 lokacin da ya yi balaguro zuwa Abuja domin cashewa.

    Mawakin tare da manajansa an tsare su ne a cikin watan Yuni bisa laifin yin balaguro a lokacin da aka takaita zirga-zirge saboda dakile yaduwar cutar korona a Najeriya.

    An ci tarar kowannensu naira dubu 100 saboda wannan laifin a zaman kotu a Alhamis.

    Lokacin da lamarin ya faru, ministan sufurin jiragen sama ya dakatar da kamfanin jiragen saman da ya dauke su daga Lagos zuwa Abuja, amma daga bisani an bar kamfanin ya cigaba da ayyukansa.

    Ga abin da gidan talabijin na Channels a Najeriya ya wallafa a shafinsa na Twitter

  17. Labaran korona a fadin duniya

    Annobar korona na ci gaba da yaduwa a duniya, duk da dai wasu kasashe na ci gaba da rayuwa kamar a baya.

    Wasu masana na cewa dole a koyi rayuwa da korona kamar yadda ake rayuwa da wasu cutukan irin su zazzabin cizon saura kyanda da dai sauransu.

    Ga wasu daga cikin labaran halin da ake ciki a fadin duniya kan cutar korona:

    ·Masu cutar korona sun haura miliyan daya a nahiyar Afrika, in ji jami’ar Johns Hopkins

    ·Afrika ta Kudu – inda a ke yin gwajin annobar sosai a fadin kasar – sun samu masu cutar sama da 500,000

    ·Haka kuma, masana na cewa karancin gwajin cutar a fadin Afrika na nufin cutar za ta iya fin halin da ake ciki muni a nan gaba

    ·An kara samun mutane 450 masu cutar korona a birnin Victoria na Australia cikin awa 24

    ·Dukkan wadanda suka shiga New South Wales daga Victoria sai sun killace kansu a otel na kwana 14 wanda kuma hakan wajibi ne ba zabi ba

    ·Sama da mutane miliyan biyu aka gwada a India aka tabbatar sun kamu da korona, in ji hukumomin kasar

    ·Kasar ta bayar da rahoton samun miliyan daya na baya-bayan nan cikin kwanaki 20 ne kacal, wanda hakan ya wuce yadda cutar take yaduwa a Amurka da Brazil.

    ·Shugaban Brazil Jair Bolsonaro ya nuna fusatarsa kan wasu masu tseren keke, wadanda suka cewa ‘yan Brazil su ci gaba da rayuwarsu. Sama da mutum 98,000 sun mutu a kasar sakamakon cutar.

  18. An kashe mutum 21 a kudancin Kaduna

    Rahotanni daga kudancin jihar Kaduna na cewa mutane kusan 21 ne aka kashe a karamar hukumar Zangon Kataf a tashin hankali na baya-bayannan a yankin.

    Kashe-kashen na zuwa ne kwanaki kadan bayan hukumomi a Najeriya sun ce sun tura karin jami’an tsaro a yankin domin kawo karshen zubar da jini.

    Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da afkuwar lamarin, inda kakakinta, ASP Mohammed Jalige ya shaidawa jaridar Daily Trust cewa mutum 21 ne suka mutu a yayin da uku suka samu raunuka.

    Rahotanni sun ce an kaddamar da hare-haren ne a wasu kauyuka hudu na karamar hukumar Zangon Kataf a daren ranar Laraba.

    Sai dai al’ummar yankin na cewa mutum 33 ne suka mutu cikin hadda kananan yara ba 21 kamar yadda ‘yan sanda suka sanar.

  19. Shugaban Ivory Coast Ouattara zai tsaya takara karo na uku

    Shugaban Ivory Coast Alassane Ouattara ya ce zai tsaya takara karo na uku a zaben da za a yi a watan Oktoba.

    A makon jiya ne jam'iyyar shugaban kasar ta tsayar da shi takara ko da yake ya ce zai yi nazari kafin ya amince.

    Mutumin da jam'iyyar ta tsayar takara a baya, Firaminista Amadou Gon Coulibaly, ya mutu sakamakon bugun zuciya ranar 8 ga watan Yuli.

    "Ni ne dan takarar shugaban kasa a zaben ranar 31 ga watan Oktoba," in ji Mr Ouattara a hirarsa da kafar watsa labarai ta RTI.

    "Na yanke shawarar jin kiran a 'yan kasa suka yi min," a cewarsa.

    Matakin shugaban kasar zai iya jawo suka saboda wa'adi biyu aka amince shugaban kasa ya yi a kan mulki.

    A baya ya ce ya kamata a bai wa sabbin jini damar shugabancin kasar, sai dai mutuwar firaiministan ta sa ya sauya matsayinsa.

    Jam'iyyar FPI ta tsohon shugaban kasar Laurent Gbagbo ta tsayar da tsohon firaiminista Pascal Affi N’Guessan a matsayin dan takatarta a zaben, abin da ya kawo rade-radin da ake yi cewa Mr Gbagbo zai sake neman shugabancin Ivory Coast.

  20. Aubameyang na dab da sabunta zamansa a Arsenal, Man Utd za ta sayar da Lingard

    Dan wasanArsenalda Gabon Pierre-Emerick Aubameyang, mai shekara 31, yana dab da sabunta kwangilar shekara uku a kungiyar.(Telegraph - subscription only)

    Manchester Unitedza ta karbi tayin sayar da dan wasanta mai shekara 27 dan kasar Ingila Jesse Lingard.(Guardian)

    Laziotana da kwarin gwiwar kammala sayen dan wasanManchester Citykuma tsohon dan wasan Sufaniya David Silva. Dan wasan mai shekara 34 zai shiga kasuwa a bazarar nan.(Sky Sports)

    Dan wasanChelseadaBrazil Willian, mai shekara 31, amince da kwangilar shekara uku aArsenalkuma za a rika ba shi £100,000 duk mako.(ESPN).

    Latsa nan don karanta cikakken labarin wasannin: