Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Mutum 135 ne suka mutu a Beirut, 5,000 sun jikkata

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya, Buhari Muhammad Fagge and Umar Mikail

  1. Amurka ta bai wa Ethiopia taimakon na'urar ventilators

    Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin na’urar taimakawa numfashi 250 ga kasar Habasha domin taimaka mata wajen yaƙi da annobar korona.

    An bayar da taimakon ne bayan wani alkawari da shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa Firaiminista Abiy ta waya a watan Afrilu.

    Jakadan Amurka a ksar Michael Raynor ya ce taimakon wani kokari na karfafa gwiwa ga mutanen Ethiopia.

    Ministan lafiya na Ethiopia Dakta Lia Tadesse ya nuna farin cikinsa da wadannan kayan aiki da aka bai wa kasarsa.

    A wata sanarwa da Amurka ta fitar ta ce za ta fitar da tsarin yadda za a yi aiki da kayan da kuma samar da horo ga ma’aikatan lafiya na Habasha domin samun kwarewa.

  2. Akwai alamun dawowar korona a karo na biyu – Afrika Ta Kudu

    Ministan lafiya na Afrika Ta Kudu Zweli Mkhize ya ce kasar na cikin hadarin fuskantar annobar korona a karo na biyu,

    Ya shaida wa taron manema labarai da ya gudana ta intanet cewa dole a ci gaba da daukar matakan kariyar da aka kakaba game da wannan cuta ta korona.

    Ministan ya ce har yanzu kasar tana da sauran gadaje da ba a yi amfani da su ba duk kuwa da cewa wasu cutar sun kai rabin miliyan a karshen sata.

    Afrika Ta Kudu ce kasar da korona ta fi girgizawa a nahiyar Afrika kuma ita ce ta biyar cikin jerin kasan shen duniya da ke fama da annobar.

    Ministan ya kuma ba da umarnin a gudanar da bincike kan wasu rahotanni da ke yawo a kafafen sadarwa da ke cewa ma’aikatan lafiya a kasar na fama da karanci kayan kariya.

    Ya kuma wallafa hakan ne a shafinsa na Twitter:

  3. Farfado da tattalin arzikin Amurka ne a gabanmu - Trump

    Shugaba Trump ya ce yana duba yiwuwar ɗaukar matakan gaggawa domin tada komaɗar tattalin arzikin ƙasar, idan har tattaunawa kan samar da tallafin rage raɗaɗin da annobar korona ta haifar ba ta samu ba.

    A wani taron manema labarai da aka gudanar a fadar White House, Trump ya ce yana duba hanyoyin taimaka wa waɗanda suka rasa aikinsu saboda cutar.

    Ana kuma yunƙurin dakatar da korar ma'aikata da ake shirinyi.

    Ministan kuɗi na ƙasar, Steve Mnuchin ya ce an samu ci gaba kan wasu mahimman abubuwa da suka shafi sabon tsarin tallafin yayin tattaunawa da manyan 'yan Dimokrat da ke majalisar dokokin Amurka ranar Talata.

    Akwai miliyoyin mutane da suka rasa ayyukansu a Amurka sakamakon wannan annoba, sashen kula da ayyukan yi na Amurka ya yi hasashen cewa marasa ayyukanyi za su iya kai wa miliyan 30 a kasar nan da wani lokaci.

    Rahotanni na cewa ana kara samun masu bukatar karbar taimako da dama a Amurka kusan ko wanne mako.

  4. Masar ta fice daga sabuwar tattauna kan Kogin Nilu

    Masar ta fice daga sabuwar tattaunawar aikin ginin samar da wutar lantarki da Habasha ke shirin yi daga kogin Nilu.

    Bijirewar bayan-bayan nan da Masar din ta yi bayan gabatar da sabbin dokokin da Habasha ta yi.

    Ita ma Sudan ta yi barazanar ficewa daga tattaunawar, tana cewa Ethiopia na kokarin tilasta ta kan sake yarjejeniyar raba ruwan Blue Nile.

    Ministan ruwa na Sudan, Yasser Abbas, ya ce ya karbi wasika daga takwaransa na Ethiopia kan bukatunsu.

    Misintan Sudan din ya ce bukatar da Habasha ta miko “ ta hadar da kokarin yadda za a raba amfani da ruwan Blue Nile. Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito.

    Masar da Habasha da kuma Sudan wadanda sune kasashen da Blue Nile ya ratsa ta cikinsu sun ta fama da tattaunawa cikin sama da shekara 10 kan yadda za su yi amfani da kogin.

    Yayin da Habasha ke murnar saukar damuna da kuma cikar kogin, makotanta na ci gaba da nuna damuwa kan makomar mutanen da suka dogara kan kogin domin rayuwa.

  5. Gobara ta yi barna a shalkwatar ECOWAS a Abuja

    Gobara ta lalata wani bangare na shalkwatar ofishin kungiyar kasashen yammacin Africa – ECOWAS a ranar Talata da daddare.

    Kawo yanzu hukumomi basu ce komai ba kan lamarin kuma ba a san iya barnar da gobarar ta yi ba.

    Sai dai wasu rahotanni na nuna cewa gobarar ta lalata bangaren ofisoshin kula da kudi na sakatariyar.

  6. Cin hanci ya sa an naɗa mataimakin shugaban kasa ministan lafiya

    An naɗa mataimakin shugaban kasar Zimbabwe Constantino Chiwenga a matsayin sabon ministan lafiya na kasar, bayan an kwashen kimanin wata daya ana ta rikicin cikin hanci da ya dabaibaye ma’aikatar kan kayayyakin kariyar cutar korona.

    Mista Chimwenga tsohon shugaban soji ne wanda ya jagoranci karbar mulki daga hannun tsohon shugaban kasar Robert Mugabe.

    Wanda ya gada a ma’aikatar lafiyar Obadiah Moyo ya bayyana gaban kotu a watan Yuni kan zargin cin hanci da rashawa da ake tuhumarsa da shi, na kuɗade da suka kai dalar Amurka biliyan 20, kan wata kwangila da aka bai wa wani kamfanin kasar Hungary wanda ake zargin ba abi ka’idar bayar da ita ba.

    An dai bayar da belin shi.

    A wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta fitar, ta ce shugaba Mnangagwa ya lura akwai bukatar daukar matakan gaggawa kan tsarin kiwon lafiyar kasar dangane da abin da ya shafi annobar korona.

    Zimbabwe na da masu korona 4,200 kuma mutum 81 sun mutu sakamakon cutar, amma da alamun wannan adadin da gwamnati ta fitar zai iya zarce hakan.

  7. Buɗewa

    Daga nan sashen hausa na BBC muke muku fatan an tashi lafiya.

    Ku kasance da mu cikin wannan rana domin samun labarai da rahotanni da dumi-duminsu. Kan abubuwan da suka shafi kasashen Afrika da sauran nahiyoyin duniya baki daya.