Ƙarshen rahotannin kenan
Jama'a mun kawo ƙarshen rahotanni kai-tsaye a wannan shafi, sai kuma gobe idan Allah ya kai mu.
Umar Mikail ke cewa mu zama lafiya.
Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.
Nasidi Adamu Yahaya, Buhari Muhammad Fagge and Umar Mikail
Jama'a mun kawo ƙarshen rahotanni kai-tsaye a wannan shafi, sai kuma gobe idan Allah ya kai mu.
Umar Mikail ke cewa mu zama lafiya.
Manchester City ta kammala ɗaukar ɗan wasan bayan Bournemouth mai suna Nathan Ake kan fan miliyan 40.
Ɗan ƙasar Netherlands wanda ya sanya hannu kan yarjejeniyar shekara biyar a Etihad, ya bayyana komawa ƙungiyar ta Guardiola a matsayin "mafarki".
"Pep Guardiola kociya ne da ake ƙunarsa a duniya baki ɗaya. Abubuwan da ya yi a harkar ƙwallo suna nuna kan su," in ji ɗan wasan mai shekara 25.
"Nasarorin da ya samu abin mamaki ne sannan salon ƙwallon da yake bugawa yana burge ni."
Hukumar kula da kafofin yaɗa labarai ta yanke sabbin hukunce-hukunce a kan wasu ‘yan jarida da wasu shugabannin kamfanonin yaɗa labarai.
Bayan ta yi zama wata biyu da suka gabata, hukumar ta ce ta samu ‘yan jarida da Shugabanninsu da rashin bin ƙa’idojin aikin jarida wurin yaɗa labarai da wallafa su.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nuna alhini da baƙn cikin rasuwar Sheikh Ahmed Tidiane Niass, Khalifa jagoran kungiyar Musulunci ta Tijjaniyya na Nahiyar Afirka.
Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban na musamman kan kafafen yaɗa labarai, Buhari Sallau ya wallafa a shaifnsa na sada zumunta.
Sanarwar ta ce cikin sakonsa na ta'aziyya zuwa ga Shugaba Macky Sall na Senagal da 'yan Senegal da ma mabiya ɗariƙar Tijjaniyya, Buhari ya ce mutuwar "abin baƙin ciki ne ga dukkaninmmu" sannan ya yi kira da a koyi da jagoran.
"Shugaban kasa ya tuno cewa a watan Yuni na shekarar 2018, Sheikh Ahmed Niass ya ziyarci fadar shugaban kasa a birnin Abuja tare da wasu fitattun 'yan Najeriya ciki har da shugaban rukunin kamfanin BUA Alhaji Abdulsamad Rabi'u," in ji sanarwar.
"A madadin ni kaina da gwamnati da kuma al'ummar Najeriya, Shugaba Buhari ya yi addu'ar samun madawwamin nutsuwa ga wannan rai da ta rasu."
A jamhuriyar Nijar, mazauna yankunan karkara ne ke kokawa da wahalhalun rayuwa da suka ce suna kawo masu cikas a kokarinsu na neman cigaba.
A yankin Tahoua da Wakiliyarmu Tchima Illa Issoufou ta ziyarta kwanakin baya, ta tattauna da wata mata da ta ce rashin wadata na hana yaransu zuwa makaranta.
Hadiza Mahamadou ta ce suna yin wasu 'yan sana'o'i na cikin gida don taimakama gidajensu.
Gwamnatin Jihar Bauchi ta ce ta ɗauki yara 49,534 a makarantun almajirai da gwamnatin tarayya ta gina a jihar.
Mallam Abdullahi Muhammad, kakakin hukumar BASUBEB ta Bauchi ne ya bayyana hakan a hirarsa da kamfanin dillancin labarai na NAN ranar Talata a Bauchi.
Ya ce an buɗe sabbin makatantun tsangaya 931 cikin shekara biyu da suka wuce domin faɗaɗawa da kuma a ƙara bai wa yara damar samun ilimi na zamani a Jihar Bauchi.
"A cikin yara 49,534 da aka ɗauka, akwai mata 14,497 da maza 35,037, yana mai cewa an kaddamar da shirin ne a cikin ƙaramar hukuma tara a na Jihar,” in ji shi.
Ɗaruruwan 'yan Lebanon sun bai wa 'yan uwansu gidajen kwana, waɗanda hatsarin abubuwan fashewa ya rutsa da su.
Sun yi ta amfani da maudu'in #OurHomesAreOpen wato "gidajemmu a buɗe suke" a shafukan sada zumunta da Larabci da Turancin Ingilishi domin neman waɗanda suke da buƙata.
"Na yi niyyar na yi wani abu a kai, duk na ɗimauce," a cewar wanda ya kafa dandalin ThawraMap, wanda ake amfani da shi domin gano wuraren zanga-zanga wanda kuma yanzu ake amfani da shi don gano inda ake da gadaje da kuma otel na kyauta.
"A yanzu mutane da yawa za su ras wurin kwana. Za su tafi wurin 'yan uwansu da abokai amma bayan kwana biyu kuma ya za su yi?" in ji wani ɗan gwagwarmaya a hirarsa da Reuters.
Tun farko gwamnan Beirut, Marwan Aboud ya ce kusan mutum 300,000 ne suka rasa mahallansu sakamakon fashewar da ta afku ranar Talata.
Ofishsin mai shigar da ƙara na Faransa ya ce 'yan ƙasar 21 ne suka jikkata a hatsarin fashewar wasu sinadarai a Bierut na Lebanon ranar Talata.
Remy Heintz ya ce an fara gudanar da bincike kan waɗanda suka jaikkata din.
Ministan Lafiya na Lebanon ya bayyana cewa mutum 135 ne suka mutu sannan wasu 5,000 suka jkkata sakamakon fashewar tan 2,750 na sinadarin ammonium nitrate - wanda ake haɗa takin zamani da shi - bayan an ajiye shi ba tare da kulawa ba a wani wurin ajiya
Ministan Lafiya a Lebanon ya bayyana babu daɗewa cewa mutanen da suka mutu sakamakon fashewar ranar Talata sun zama 135 tare da jikkata wasu 5,000, a cewar kafar Al Manar TV.
har yanzu akwai adadin mutanen da ba a san inda suke ba, in ji shi.
Ga abubuwan da muka sani game da fashewar sinadarai a Beirut na Lebanon ranar Talata zuwa yanzu:
Yau al'umar Sri Lanka za su kaɗa ƙuri'a domin zaben sabbin 'yan majalisa inda aka tanadi matakan kariya domin hana bazuwar cutar korona.
Shugaba Gotabaya Rajapaksa na fatan ƙoƙarin da yake wajen yaƙi da annobar ta korona zai taimaka wa jam'iyyarsa ta samu nasara.
Idan har jam'iyyar ta lashe kashi biyu bisa uku na kujerun majalisar, hakan zai ƙara wa shugaban ƙarfi kan madafun iko.
Sai dai akwai fargaba cewa hakan zai bai wa Mista Rajapaksa da iyalinsa da ke fuskantar zarge-zargen cin hanci da take hakkokin bil adama iko sosai.
Ƙarin wasu 'yan Najeriya 306 sun isa Abuja babban birnin ƙasar daga ƙasar Daular Larabawa wato UAE da misalin ƙarfe 08:44 na safiyar Laraba.
An ɗebo su ne sakamakon maƙalewa da suka yi a ƙasashen waje saboda matakan da ake ɗauka na daƙile yaɗuwar korona.
Hukumar 'yan Najeriya mazauna ƙasashen waje ta NIDCOM ta bayyana cewa wasu daga cikinsu za su sauka a Abuja, wasu kuma su wuce Legas.
Dukkaninsu gwaji ya nuna ba sa ɗuke da cutar a cewar hukumar sannan kuma za su killace kansu na tsawon mako biyu.
Gwamna Aminu Bello Masari na Jihar Katsina ya kai wa Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ziyara a Fadar Shugaban Ƙasa ta Aso Rock da ke Abuja.
BBC ba ta samu ƙarin bayani ba game da abin da shugabannin biyu suka tattauna. Sai dai idan ba a manta ba Jihar Katisna na shan fama da matsalolin tsaro da suka haɗa da hare-haren 'yan fashin daji.
A baya dai gwamnatin jihar ta ƙulla yarjejeniya da wasu daga cikin ƙungiyoyin maharan, sai dai da alama hakan bai hana su ci gaba da kashe mutane babu gaira babu dalili ba.
Fadar shugaban ƙasar ta sha bayyana cewa sojojin ƙasar sun ƙaddamar da ayyukan kakkaɓe miyagun a ƙarƙashin rundunar Operation Hadarin Daji, inda sojojin ke cewa suna cin galaba a jihohin Zamfara da Katsina da Sokoto.
Ƙarin wani kamfanin sufurin jirgin sama ya kori matuƙa da kuma injiniyoyi 100 a ci gaba da faɗi-tashin da ɓangaren sufurin yake yi sakamakon annobar korona.
Kamfanin Bristow Helicopters ya fuskanci matsi sakamakon annobar ta korona kuma ya ce matakin ba mai sauƙi ba ne, wanda ya zama dole ya ɗauka yayin da yake ta ƙoƙarin yin garambawul ga ayyukansa.
Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗn bayan ɗaya daga cikin manyan kamfanonin jirage a Najeriya - Air Peace - ya dakatar da matuƙa jiorgin kusan 70 sannan ya rage albashin ma'aikata.
Kamfanonin sufurin jiragen helikwafta na samun kwastomomi ne akasari ta hanyar aiki da ɓangaren man fetur da iskar gas a Najeriya.
Gwamnatin Najeriya ta ce daga yanzu duk mutumin da aka samu da laifin yin kalaman kiyayya zai biya tarar Naira miliyan biyar, wato kari sau dari kenan kan tarar da a baya aka sanya kan wannan laifi.
Ministan watsa labaran kasar Alhaji Lai Mohammed ne ya bayyana hakan ranar Talata a Abuja babban birnin kasar, lokacin da yake kaddamar da kwaskwarimar da aka yi wa dokar watsa labarai ta kasar.
Ya ce ya dauki matakin ne bayan samun amincewar Shugaban kasa Muhammadu Buhari wanda ya bukaci a sauya dokar sakamakon irin kalaman kiyayya da 'yan kasar suka rika yi a lokaci da kuma bayan babban zaben kasar na 2019.
Ministan lafiya na Afghanistan ya ce samfuran da aka dauka sun nuna kusan kashi daya cikin uku na yawan al'ummar kasar wanda ya kai miliyan 10 na dauke da korona.
An kaddamar da binciken ne watanni biyu baya tare da taimakon WHO da kuma jami'ar Johs Hopkins.
A mafi yawan lokuta, jami'an da suka kamu basa nuna alamun cutar kuma abu ne mawuyaci sun iya gano ta.
Wani gwajin gama-gari da aka yi ya nuna cewa sama da kashi 50 cikin 100 na mazauna babban birnin Kabul sun kamu da cutar.
Akwai a kalla mutum dubu36 da aka tabbatar suna dauke da cutar akwai kuma sama da mutum 1,200 da suka mutu ya zuwa yanzu.
Sama da mutum 700,000 ne suka rasa rayukansu sakamakon annobar korona a fadin duniya, kamar yadda jami'ar Johs Hopkins mai bibiyar kididdigar korona ta bayyana.
An fi samun mamatan a Amurka, inda take da mutum (156,830) da suka mutu, sai Brazil da take biye mata da adadin wadanda suka mutu (95,819), Mexico na ta uku da mutum (48,869), a Burtaniya mutum (46,295) ne suka mutu sai kuma India da ke da (39,795).
Yana da muhimmanci a gane cewa ba zai yiwu a kwatanta kasashe duka da ma'auni daya ba, saboda banbancin da ke akwai wajen yadda suke gwajin cutar da kuma yadda wasu ke kirga wadanda suka mutu dalilinta.
Banbancin yawan al'umma na da muhimmanci yayin kwantanta kasashen.
Burtaniya na da mutane mikiyan 66, yayin da India ke da mutane biliyan daya da digo uku.