Cutar korona ta yi kisa mafi girma a Afirka ta Kudu
Afirka ta Kudu ta bayyana cewa cutar korona ta kashe mutum 572 a cikin kwana guda, wanda shi ne adadi mafi girma tun da cutar ta barke a kasar.
Cutar ta kashe mutanen ne ranar Laraba, inda yanzu jimulla mutum 5,940 suka mutu sanadin cutar a Afirka ta Kudu.
Kusan rabin mutanen da suka mutu suna zaune ne a lardin Western Cape.
Sai dai galibin mutanen da suka kamu da cutar suna zaune a lardin Gauteng province, cibiyar kasuwanci kuma inda cutar ta fi kamari a kasar.
Lardin na Western Cape shi ne na biyu a mafi yawan mutanen da suka kamu da cutar korona a Afirka ta kudu.
Kasar ta tabbatar cewa mutum 394,948 suka harbu da korona.