Sai 'yan Najeriya sun so za a kawo ƙarshen rashin tsaro – Buratai
Shugaban Rundunar Sojojin Ƙasa ta Najeriya, Janar Yusuf Tukur Buratai ya ce 'yan Najeriya za su iya kawo ƙarshen matsalolin tsaro da kansu tun da "su ne suke zaune da 'yan bindigar".
Buratai ya faɗi haka ne ranar Litinin jim kaɗan bayan ya gana da Shugaba Muhammadu Buhari a fadarsa, inda ya ce 'yan ƙasa ba sa ba su goyon baya ta hanyar ba su bayanai amma suna zargin jami'an tsaro da gazawa.
Kafafen yaɗa labarai a Najeriya sun ruwaito shi yana cewa satar mutane da garkuwa da su, da fashi da ta'addanci za su zo ƙarshe ne kawai idan 'yan Najeriya sun ga dama.
Kazalika Buratai ya ce kashi 99 cikin 100 na miyagun 'yan Najeriya.
Magajin Garin Batsari da ke Jihar Katsina, Alhaji Tukur Mu'azu Ruma ya faɗa wa BBC cewa an mayar da mata kusan 600 zawarawa a garin nasa, yayin da yara kusan 2,000 suka zama marayu.
Buratai yana wannan batu ne yayin da aka kashe aƙalla mutum 192 cikin wata uku da suka gabata a Najeriya, a wani bincike da jaridar Daily Trust ta gudanar.