Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Amurka na tuhumar China kan leken asiri ta intanet kan riga-kafin Covid-19

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya and Umar Mikail

  1. Rufewa

    Jama'a a nan muka kawo karshen labarai da rahotanni kai tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Daga cikin labaran da muka wallafa muku akwai:

    • Majalisar Dattawa ta bukaci a sauke hafsoshin tsaron Najeriya
    • Mutum 229 sun mutu a Iran cikin awa 24
    • Jana'izar Isma'ila Isa Funtua kai-tsaye
    • Sai 'yan Najeriya sun so za a kawo ƙarshen rashin tsaro – Buratai
    • An kashe mutum tara a wani sabon hari a Kaduna
    • Buhari ya gwale 'yan Majalisar Dattawan Najeriya
    • Gwamnatoci a Birtaniya sun gaza kare ƙasar daga barazanar tsaro daga Rasha – Rahoto
    • Trump ya yi barazanar tura ƙarin 'yan sandan tarayya zuwa jihohi
    • Abin da ya kai Jonathan fadar Shugaba Buhari
    • Ma'aikaciyar jinya ta farfaɗo bayan kwana 40 a sume sakamakon cutar korona
    • Zimbabwe za ta kara santya dokar hana zirga-zirga a kan corona
    • Amurka ta buƙaci ƙasashen duniya su yaƙi jam'iyyar kwaminisanci ta China
    • Nijar za ta sayar wa Najeriya tataccen man fetur
    • Amurka na tuhumar China kan leken asiri ta intanet kan riga-kafin Covid-19
    • Igiyar ruwa mai karfi ta tsaga jirgin ruwan dakon kaya a Kamaru

    Kuna iya zuwa can kasan shafin don karanta labaran da muka wallafa a yau.

    Sai ku kasance da mu gobe da safe don sake jin halin da duniyar ke ciki.

  2. 'Yan sanda sun damke matasa wadanda suka kashe wata bayan sun yi mata fyade

    Rundunar ‘yan sanda a jihar Katsina a Najeriya ta ce ta kama wasu mutane biyu da ta jima tana nema kan zarginsu da yi wa wata matar aure fyade, suka kuma koma suka kashe ta daga bisani, da za ta tona su.

    Lamarin dai ya faru ne a watan Mayu a wani kauye da ke karamar hukumar Bakori ta jihar.

    Rundunar ta bayyana damke mutanen ne kwana daya bayanwata nasarar da ta ce ta yi kuma ta kama wani mutum mai shekara 51 da ake zargi da lalata kananan yara mata ciki har da mai shekara hudu.

    Kakakin rundunar ‘yansandan ta jihar Katsina, SP Gambo Isa wanda ya tabbatarwa da BBC ya ce za su ci gaba da aiki domin ganin an kawo karshen aikata miyagun laifuka a jihar.

    A cikin ‘yan watannin nan an samu karuwar masu aikata fyade da lalata kananan yara a arewacin Najeriya.

  3. Igiyar ruwa mai karfi ta tsaga jirgin ruwan dakon kaya a Kamaru

    Wata Igiyar ruwa mai karfi ta tsaga wani jirgin ruwa na daukar kaya a garin Idenau a lardin kudu maso yamma a Kamaru.

    Sai dai ba a samu asarar rayuka ba, sai dai dimbin asarar kayan haja da tsabar kudade na ‘yan kasuwa.

    Wannan jirgin kuma ya taso ne daga Calabar a Najeriya zuwa Idenau a Kamaru.

    Ana cewa lalacewar da injunan jiragen suka yi ne ya janyo tsagewar da ya yi.

    Ku saurari rahoton Mohamman Babala ta hanyar latsa alamar lasifikar da ke kasa:

  4. Amurka na tuhumar China kan leken asiri ta intanet kan riga-kafin Covid-19

    Hukumar Shari'a Ta Amurka ta zargi China da daukar nauyin masu kutse da ke hakon dakunan gwaje-gwajen da suke aikin samar da riga-kafin cutar korona.

    Jami'ai sun tuhumi wasu 'yan China biyu da ake zargi da leken asiri kan kamfanonin Amurka da ke bincike kan cutar korona suka kuma samu taimako daga wakilan jihohi kan sauran abubuwan da suka sata.

    Tuhumar na zuwa ne a yayin da Amurka ke tsaka da binciken kutsen da China take yi a intanet.

    A makon da ya gabata Burtaniya da Kanada suka zargi Rasha da kokarin satar binciken da ya shafi Covid-19.

    A ranar Talata ne aka fitar da zargin da ake yi wa daliban da ke karatun injiniya Li Xiaoyu da Dong Jiazhi tare da tuhumar su kan shirya tuggun satar da bayanai da kutse a intanet.

  5. Nijar za ta sayar wa Najeriya tataccen man fetur

    A jamhuriyar Nijar yarjejeniyar kasuwanci ce aka kulla tsakanin kamfanin man fetur na Najeriya NNPC da kamfanin dillancin man fetur na Nijar SONIDEP, kan batun saida wa Najeriyar tataccen man da za ta yi amfani da shi cikin gida.

    Wannan dai ba ita ce yarjejeniyar farko ba da kasashen biyu suka kulla kan wannan batu ba, sai dai wannan karon za su dauki kwararan matakai don ganin yarjejeniyar ta mike.

  6. Amurka ta buƙaci ƙasashen duniya su yaƙi jam'iyyar kwaminisanci ta China

    Sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo ya bukaci dukkanin kasashe da su yi karfin hali, su tashi tsaye, su ki, tare da yakar jam'iyyar Kwaminisanci ta China.

    Ya bayyana haka ne bayan da ya yi wata tattaunawa da Firaministan Burtaniya Boris Johnson da kuma Dominic Raab, Sakataren Harkokin Wajen Burtaniyar a Landan.

    Da yake jawabi yayin wani taron manema labarai a Ma'aikatar Harkokin Wajen Burtaniyar, Mista Pompeo, ya yaba wa Burtaniyar kan daukar matakin hana kamfanin Huawei na China shiga tsarin samar da intanet dinta mai karfin 5G, me sauri kamar kiftawar ido.

    Bugu da kari, Mista Pompeon ya yi maraba da matakin gwamnatin Boris Johnson din a kan sabuwar dokar tsaro ta China a Hong Kong.

  7. Zimbabwe za ta kara santya dokar hana zirga-zirga a kan corona

    Shugaba Zimbabwe, Emmerson Mnangwagwa ya umarci jami'an tsaron kasar da su sanya dokar takaita zirga-zirga tun daga safe har faduwar rana daga ranar Laraba.

    Ya ce yin hakan ya zama dole saboda a takaita yaduwar cutar korona a kasar wadda ta yi sanadiyyar rasa rayukan mutum 26 da kuma kama wasu mutum kusan dubu biyu.

    An dai umarci 'yan kasar da su kasance a gida in dai ba sayan abinci da ruwa da kuma kayan muhimman bukatu za su yi ba kamar magani da dai sauransu.

    To sai dai kuma tuni aka shirya gudanar da wasu jerin zanga-zanga a kan yin bore ga gwamnati inda kungiyoyin hamayya suka ce wannan dokar takaita zirga-zirgar da aka sanya an yi ta ne saboda a hana su yin zanga-zangar wadda za a yi a kan yadda ake samun cin hanci da rashawa da kuma almubazzaranci da kudaden gwamnati a tsakanin jami'an gwamnatin kasar.

  8. Ma'aikaciyar jinya ta farfaɗo bayan kwana 40 a sume sakamakon cutar korona

    Wata ma'aikaciyar jinya da ta shafe kwana 40 a sume bayan ta kamu da cutar korona ta yi ban kwana da asibiti cikin yanayi mai ban tausayi tsakaninta da abokan aikinta.

    Ayesha Orlanda mai shekara 52 kuma babbar ma'aikaciyar jinya a asibitin Bradford Royal Infirmary da ke arewacin Ingila, ta kasance a ɓangaren kulawar gaggawa tsawon kwana 41 a asibitin bayan an kai ta a watan Mayu.

    Ta sha fama da jinya amma ta ce yanzu ta samu dama "karo na biyu a rayuwa".

    Abokan aikin Orlanda sun riƙa tafa mata lokacin da take barin asibitin.

  9. Abin da ya kai Jonathan fadar Shugaba Buhari

    A yau tsohon Shugaban Najeriya Goodluck Ebele Jonathan ya kai wa Shugaba Muhammadu Buhari ziyara a fadarsa da ke Abuja, inda suka tattauna a wata ganawar sirri.

    Saƙon Twitter da Buhari ya wallafa ya nuna cewa Jonathan ya je Fadar Aso Rock Villa domin miƙa rahoton aikin sasanta rikicin siyasa ne wanda ƙungiyar ECOWAS ta tura shi ƙasar Mali a makon da ya gabata ga Buhari.

    "Na karɓi rahoton wakilin ECOWAS na musamman a Mali, tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan, game da rikicin siyasar Mali kuma za mu nemi shugaban ƙungiyar, Shugaban Nijar, ya yi mana cikakken bayani a matsayinsa na shugaba," in ji Buhari.

    A jawabin da ya gabatar bayan ganawa da Buhari, Jonathan ya ce ƙungiyar haɓaka tattalin arzikin yankin Afirka Ta Yamma ba za ta taɓa goyon bayan tsige wani zaɓaɓɓen shugaba ba.

    Tsohon shugaban yana magana ne kan kiraye-kirayen da 'yan adawa suka riƙa yi ga Shugaban na Mali, Ibrahim Boubacar Keita da ya sauka daga muƙaminsa.

    Goodluck Jonathan ya ce idan aka cire zaɓaɓɓen shugaba za a samu "rashin doka da oda a ƙasashe" sannan ya ce hatta AU - ƙungiyar haɗin kan ƙasashen Afirka - ba za ta yi haka ba.

  10. Trump ya yi barazanar tura ƙarin 'yan sandan tarayya zuwa jihohi

    Shugaban Amurika Donald ya yi barazanar tura ƙarin dakarun gwamnatin tarayya domin kawo ƙarshen zanga-zanga a biranen ƙasar.

    Mista Trump ya soki garuruwa da yawa, waɗanda 'yan jam'iyyar Democrat ke jagoranta ranar Litinin - da suka haɗa da Chicago da New York - yana mai cewa shugabannin suna tsoron ɗaukar mataki.

    Ya kuma ce jami'an tsaron da aka tura Oregon "sun yi aiki irin wanda ake so" don dawo da doka da oda a Portland.

    'Yan Democrat sun zargi Trump da ƙoƙarin yin amfani da hakan domin yin kamfe a yankunan da jam'iyyarsa ba ta da ƙarfi.

  11. Gwamnatoci a Birtaniya sun gaza kare ƙasar daga barazanar tsaro daga Rasha – Rahoto

    Wani kwamitin majalisar dokokin Birtaniya ya gano cewa gwamnatocin da suka gabata sun gaza kare dimokuraɗiyyar ƙasar daga barazanar tsaro daga ƙasar Rasha.

    Wakilan kwamitin tattara bayanan sirri da kuma tsaro sun ce wannan barazana ta kunshi komai sannan kuma tana da manufar yada bayanan karya da cusa kiyayya a tsakanin 'yan kasar.

    A cikin wani rahoto, kwamitin ya ce gwamnatin Birtaniya ba ta duba irin barazanar da Rasha ke yi a kan batun kuri'ar jin bahasin jama'a ba a kan 'yancin yankin Scotland.

    Wakilin BBC ya ce kutsen Rasha abu ne da za a iya cewa ya zama jiki a yanzu, amma kuma gwamnatin Birtaniya da kuma hukumomin leken asirin kasar ba su mayar da hankali akai ba, abinda ya janyo fitar da wannan rahoto na kwamitin ke nan.

    Jama'a da dama dai na tsammanin kwamitin ya amsa cewa ko Rasha ta yi kuste a bangaren dimokradiyyar Birtaniyar.

  12. Labarai da dumi-dumi, Buhari ya gwale 'yan Majalisar Dattawan Najeriya

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gwale 'yan majalisar dattawan kasar inda ya ki yarda da kiran da suka yi masa ya sauke hafsoshin tsaron kasar.

    A wata sanarwa da fadar shgaban kasar ta wallafa a shafinta na Twitter, ta ce nadawa da sauke hafsoshin tsaron yana hannun shugaban kasa don haka shi kadai ne zai yanke hukunci a kan makomarsu.

    "Ranar Talata, majalisar dattawa ta amince da da kudurin da ya yi kira ga hafsoshin tsaro su sauka daga mukamansu ko kuma a cire su saboda tabarbarewar tsaron kasar.

    "Fadar shugaban kasa ta yi duba ga wannan kuduri, kuma tana jaddada cewa nadawa da cire hafsoshin tsaro alhakin shugaban kasa ne, kuma Shugaba Muhammadu Buhari, a matsayinsa na Kwamadan rundunar sojin Najeriya, zai yi abin da ya fi wa kasar nan alfanu."

  13. An kashe mutum tara a wani sabon hari a Kaduna

    Rahotanni daga Jihar Kaduna a Najeriya na cewa 'yan bindiga sun sake kai hari a kudancin jihar a daren Talata, inda aka kashe mutum tara.

    Harin na zuwa ne ƙasa da sa'a 24 bayan kashe aƙalla mutum 18 aka kuma jikkata wasu kimanin 30 yayin shagalin aure a ƙauyen Kukum-Daji da ke Ƙaramar Hukumar Ƙaura.

    Shugaban ƙungiyar al'umar kudancin Kaduna ta SOKAPU, Honourable Jonathan Asake ya shaida wa BBC cewa 'yan bindigar sun kai harin ne a ƙauyen Gora-Gan da ke Ƙaramar Hukumar Zangon-Kataf ranar Litinin da dare, inda suka kashe aƙalla mutum tara.

    Sai dai har zuwa yanzu ba mu kai ga jin ta bakin hukumomi a jihar ta Kaduna ba. Muna fatan ji daga gare su nan gaba.

  14. Majalisar Dattawa ta bukaci a sauke hafsoshin tsaron Najeriya

    Majalisar Dattawan Najeriya ta yi kira ga manyan hafsoshin tsaron Najeriya su ajiye muƙamansu a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro a ƙasar.

    Sanata Ali Ndume ne ya gabatar da ƙudurin a lokacin zaman majalisar na ranar Talata.

    A cewar Sanata Ndume, ya gabatar da kudurin ne saboda irin yadda aka yi wa sojoji kwanton-ɓauna a Katsina inda aka kashe da dama daga cikinsu.

    Sannan kuma ga wasu sojoji da suka yi murabus daga aiki.

    A cewar Sanata Ndume waɗannan batutuwan biyu na da matukar tayar da hankali.

  15. Jana'iza kai-tsaye a Facebook

  16. Mutum 229 sun mutu a Iran cikin awa 24

    Iran ta bayar da rahoton mutuwar mutum 229 a cikin awa 24 da suka gabata sakamakon cutar korona - adadi mafi yawa kenan tun bayan ɓarkewar cutar a ƙasar.

    Sima Sadat Lari, mai magana da yawun Ma'aikatar Lafiya ta ce jumillar adadin waɗanda suka mutun sun kai 14,634 da kuma 278,827 da suka harbu da ita a Iran.

    Ƙasar ta funskanci ƙaruwar masu kamuwa da cutar tun bayan da ta sassauta dokokin kulle a tsakiyar watan Afrilu domin farfaɗo da tattalin arzikinta, wanda dama yake fama da takunkumin da Amurika ta ƙaƙaba masa.

    Shugaba Hassan Rouhani ya faɗa a farkon watan nan cewa Iran ba za ta iya sake rufe harkokin kasuwancinta ba kuma ya shawarci Iraniyawa da su saka takunkumi da kauce wa cunkoson jama'a.

  17. Kai-tsaye a Facebook

    Yadda jana'izar Isma'ila Isa Funtua ke gudana kai-tsaye a shafimmu na Facebook

  18. Daga cikin waɗanda suka halarci jana'izar har da Nuhu Ribadu

  19. Labarai da dumi-dumi, An bai wa Ministan Neja Delta kwana biyu ya bayyana sunayen 'yan majalisar da aka bai wa kwangila

    Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya, Femi Gbajabiamila ya bai wa Ministan Harkokin Yankin Neja Delta, Sanata Godswill Akpabio, kwana biyu ya wallafa sunayen 'yan majalisar da Hukumar Raya Yankin Neja Delta (NDDC) ta bai wa kwangiloli.

    Femi ya bayar da umarnin ne a zaman majalisar na yau Talata, inda ya ce matuƙar ministan ya gaza yin hakan to majalisar za ta yi amfani da dukkanin ƙarfin ikonta don tabbatar da ya yi hakan.

    A jiya Litinin ne Minista Godswill Akpabio ya faɗa wa kwamitin Majalisar Dattawa da ke bincike kan almubazzaranci da ake zargin NDDC da yi cewa mafi yawan kwangilar da hukumar ta bayar 'yan majalisar ƙasa aka bai wa.

    Da aka tambaye shi yadda 'yan majalisar suka amfana, Akpabio ya ce: "Yanzun nan na faɗa muku cewa muna da takardun da za su tabbatar da cewa akasarin kwangilolin NDDC 'Yan Majalisar Tarayya aka bai wa."

  20. Jana'izar Isma'ila Isa Funtua kai-tsaye

    Yanzu haka ana gudanar da jana'izar aboki kuma makusancin Shugaba Muammadu Buhari a Masallacin Shehu Shagari da ke Area 1 a Abuja.