Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

An saki Ibrahim Magu dakataccen shugaban EFCC

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya, Buhari Muhammad Fagge and Umar Mikail

  1. An kashe Fahim Saleh mai kamfanin Gokada a New York

    Ƴan sandan New York sun sanar da cewa an kashe Fahim Saleh, mai kamfanin Gokada a wani gida da ke Manhattan na birnin.

    Wakilin BBC Kunle Falayi ya ruwaito cewa ƴar uwar Mista Saleh ce ta gano gawarsa ranar Talata.

    Kakakin Ƴan Sandan na New York ya ce bayan an kashe shi, an kuma daddatsa gawarsa da wani zarto mai amfani da lantarki wanda ƴan sandan suka taras a kusa da gawar mamacin.

    Mista Saleh ya kafa kamfanin Gokada - kamfanin da ke samar da baburan haya a Najeriya cikin birnin Legas a 2018 - wanda ya kawo sauyi ta fuskar fasahar zamani ga harkar sufuri a babban birnin kasuwancin Najeriya.

    Jarin kamfanin ya kai dala miliyan 5.3 a lokacin da ya fara aiki cikin watan Yunin 2019.

  2. Chelsea za ta biya euro 100m kan Oblak, PSG na son ɗauko Rashford

    Chelsea ta amince ta biya euro 100m domin dauko golan Atletico Madrid dan kasar Slovenia Jan Oblak, mai shekara 27.(AS - in Spanish)

    Paris St-Germainta mayar da dauko dan wasan Manchester United da Ingila Marcus Rashford, mai shekara 22, a matsayin babban abin da ta sanya a gaba.(Independent)

    Barcelona ta amince ta ba da dan wasan Brazil Philippe Coutinho, mai shekara 28, ga Arsenal ko Newcastlea yayin da take neman kudin dauko dan wasan Inter Milan da Argentina Lautaro Martinez, mai shekara 22.(Goal)

    Dan wasan Brazil Neymar, mai shekara 28, yana so ya koma Barcelona,kuma tuni Paris St-Germain ta soma auna darajarsa ganin cewa saura shekara biyu ya kammala kwangilarsa.(Mundo Deportivo - in Spanish).

    Latsa nan don karanta karin labaran musayar 'yan kwallon kafa.

  3. Ministan Afirka ta Kudu ya kamu da cutar korona

    Ministan makamashi na Afirka ta Kudu, Gwede Mantashe, da mai dakinsa sun kamu da Covid-19.

    Ma'auratan biyu sun killace kansu amma ministan zai ci gaba da aiki daga gida, a cewar sanarwar da majalisar zartarwar kasar ta fitar.

    Wannan ne karo na uku da aka yi wa Mr Mantashe tun da annobar korona ta barke a kasar.

    Sanarwar ta kara da cewa: "Ministan ya bukaci dukkan ma'aikatansa su je a yi musu gwaji."

    An tabbatar mutum 287,000 sun kamu da cutar korona a Afirka ta Kudu, a cewar Hukumar Lafiya ta Duniya, kuma ita ce kasar da ta fi yawan masu cutar a Afirka.

  4. Barkanmu da ranar Laraba

    Ma'aikatan Sashen Hausa na BBC na yi muku barka da warhaka.

    Muna fatan za ku kasance tare da mu tsawon wannan rana domin sanin halin da duniya take ciki.

    Za mu kawo muku labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku, musamman kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da makwabtansu, har ma da sassan duniya.

    Kuna iya tafka muhawara da bayyana ra'ayoyinku a shafukanmu na sada zumunta da muhawara a BBC Hausa.