Sabuwar dambarwa a APC a yayin da Giadom ya ce shi ne shugaban riko
An shiga rudu a jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya bayan da mataimakin babban sakataren jam’iyyar na kasa, Victor Giadom ya bayyana kansaa matsayin sabon shugaban jam’iyyar na riko.
Matakin Mr Giadom ya ci karo da sanarwar da uwar jam’iyyar APC ta kasa ta fitar inda ta bayyana, tsohon gwamnan jihar Oyo, Abiola Ajimobi a matsayin shugaban jam’iyyar na riko.
Jam’iyyar APC a cikin wata sanarwa da kakakinta Malam Lanre Issa-Onilu ya fitar, ta ce Ajimobi ne zai dare kujerar shugabancin jam’iyyar.
Rahotanni sun ce Mr Giadom ya yi jawabi ga manema labarai a shalkwatar jam’iyyar na kasa a Abuja yau da safe, inda kuma ya ce ya soke wasu daga cikin hukunce-hukunce da Oshimole ya dauka.
Wannan dambarwar na zuwa ne kasa da kwana guda bayan kotun daukaka kara a Abuja tatabbatar da dakatar da Adams Oshiomole a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasa.