Wani kamfanin jirgi a NAjeriya ya bai wa ministan zirga-zirgar jiragen sama hakuri kan kai fitaccen mawakin nan Naira Marley Abuja da ya yi daga Legas a ranar Asabar, don gudanar da wata kalankuwa.
Ministan ya dakatar da Kamfanin na Executive Jet kan abin da ya kira yin zirga-zirgar da ba ta zama ta wajibi ba wanda hakan kin bin umarnin gwamnati ne da ta sanya na dakile yaduwar cutar korona a kasar.
A wata wasikar neman afuwa da ya tura wa ministan zirga-zirgar jiragen saman, shugaban kamfanin Sam Iwuajoku, ya ce an tanadi jirgin ne don bulaguron wani alkali a ranar Lahadi, wanda daga baya ya sauya shirin tafiyar tasa.
A cikin wasikar Mr Iwuajoku ya ce ya bayar da umarnin tafiyar jirgin ne a ranar Asabar bayan da ya ga sunayen fasinjojin kuma ya ga akwai wani minista a cikin jerin.
''Na ga sunan wani Fashiola Babatunde, na zaci Ministan Ayyuka ne da jama'arsa, don haka sai muka yanke shawarar tafiyar jirgin saboda bai wa ministan dama, ban san cewa taron mashiririta ba ne,'' a cewar Mr Iwuajoku said.
Fitaccen mawakin kasar Azzez Fashola, wanda aka fi sani da Naira Marley, na daga cikin wadanda jirgin ya dauka har.
Wata kafar yada labarai ta wallafa wasikar ban hakurin da kamfanin ya aike wa ministan a shafinta na Twitter: