Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Elrufa'i ya buɗe iyakokin Kaduna

Wannan shafi yana kawo muku labarai da rahotannin abubuwan da ke faruwa a duniya game da cutar korona da ma wasu labarai da suka shafi rayuwarku.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya, Buhari Muhammad Fagge, Umar Mikail and Awwal Ahmad Janyau

  1. COVID-19: Za a tursasa wa mutane sanya takunkumi a Ghana

    Shugaba Nana Akufo-Addo na Ghana ya sanar da cewa daga yanzu wajibi ne 'yan kasar su rika sanya takunkumin rufe fuska a bainar jama'a sannan ya umarci 'yan sanda su tabbatar an bi wannan umarni.

    Adadin masu kamuwa da cutar korona ya kusa kai wa 12,000, a kasar yayin da kuma mutum 54 suka mutu sannan aka gano mutum 4,000 na dauke da cutar.

    A jawabin da ya yi ta gidan talabijin na kasar, Shugaba Akufo-Addo ya ce an samu karin masu kamuwa da cutar ne saboda an inganta yadda ake gudanar da gwajin kuma hakan ya nuna cewa cutar tana ci gaba da yaduwa.

    An sassauta dokar hana tarukan addini kuma an sake bude makarantu ga daliban ajin karshe. Za a ci gaba da rufe iyakokin kasar.

    Ya zuwa yanzu mutum 250,000 aka yi wa gwaji a kasar da ke da yawan mutane miliyan 30.

  2. Likitoci sun tsunduma yajin aiki a Najeriya

    Daya daga cikin manyan kungiyoyin kwadago na likitoci a Najeriya ta ce ta soma yajin aiki ranar Litinin saboda rashin isasshen albashi da kuma kayan kariya musamman ga likitocin da ke yaki da cutar korona.

    Gamayyar Kungiyoyin Likitoci masu neman kwarewa ta ce za ta daina aiki daga Litinin ciki har da na gaggawa da kula da masu cutar korona.

    Shugaban kungiyar, Aliyu Sokomba, ya ce gwamnati ta gaza cika sharudan da aka gindaya mata, wadanda suka hada da kira da ta kara albashi ga likitocin da ke cikin kasadar kamuwa da cutar korona.

    Mutum fiye da 15,000 suka kamu da Covid-19 yayin da mutum 400 suka mutu, a cewar hukumar yaki da cutuak masu yaduwa ta kasar, NCDC.

  3. Cutar korona ta sake ɓulla a China

    An sami sabbin mutum 36 da suka kamu da cutar korona a Beijing, babban birnin China a yayin da ake fargabar cewa cutar ta sake komawa ƙasar.

    Lamarin ya faru ne ranar Asabar. An kwashe fiye da kwana 50 ba a samu bullar cutar a birnin ba gabanin lamarin da ya faru ranar ta Asabar.

    Hukumomi sun kulle ƙarin unguwanni goma a Beijing, a ƙoƙarinsu na shawo kan cutar.

    Ana alaƙanta lamarin na baya-bayan nan da wata babbar kasuwar dillancin kayan abinci.

    Wani jami'in gunduma Li Junjie ya ce an gano mutanen da suka sake kamuwa da korona a wata kasuwa ta biyu, cikin lardin Haidian.

    Ya ce za a rufe kasuwar da wasu makarantu da ke kusa, yayin da aka faɗa wa mutanen da ke rayuwa a yanki goma daf da wurin su zauna a gida.

  4. Barkanmu da wannan safiya

      • Marubuci, Nasidi Adamu Yahya
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Hausa, Abuja

    Nasidi Adamu Yahaya ne yake yi muku barka da wanna safiya.

    Da fatan za ku kasance da mu domin sanin halin da duniya ke ciki.

    Za mu kawo labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku, musamman daga kasashen Najeriya da Nijar da ma wasu sassan duniya.

    Kuna iya tafka muhawara da bayyana ra’ayoyinku a shafukanmu na sada zumunta a BBC Hausa.