Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Ƙasashen duniya sun kashe kusan tiriliyan 10 kan cutar korona – IMF

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi annobar korona na ma karin wasu daban.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya, Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Kasuwar saye da musayar 'yan kwallon kafa

    Borussia Dortmund za ta sayar da dan wasan Ingila mai shekara 20 Jadon Sancho a kan £115m.(Telegraph)

    Paris St-Germain tana son dauko dan wasan Ivory Coast mai shekara 27,Wilfried Zaha.(90 Min)

    Southampton tana shirin sabunta kwangilar dan wasan Ingila Ryan Bertrand, mai shekara 30, a yayin daLeicestertake zawarcin dan wasan.(Daily Mail)

    Golan Poland Bournemouth Artur Boruc, mai shekara 40, dan dan wasan tsakiya na Ingila Andrew Surman, mai shekara 33, da takwarorinsa masu tsaron baya Simon Francis, mai shekara 35, da Charlie Daniels, mai shekara 33, na shirin sanya hannu kan kwangilar gajeren lokaci.(Bournemouth Echo)

  2. Kada a rika ba 'yan majalisar Najeriya albashin wata-wata - Ndume

    Wani dan Majalisar Dattawan Najeriya, Mohammed Ali Ndume, ya yi kira ga gwamnatin kasar da ta mayar da aikin majalisa irin na aikatau wato idan ka yi a biya ka.

    Ya ce gwamnati tana kashe sama da kashi 70 na kasafin kudinta wajen biyan albashin ma'aikata, don haka ya kamata a rage irin ayyukan da suke yi daga wata-wata zuwa wasu kwanaki sannan a rika biyansu kudi daidai da aikin da suka yi na iya kwanakin.

    Latsa alamar lasifika da ke kasa don sauraren hira da Sanata Ndume:

  3. Mutum 104 sun kamu da korona a wani kamfani a Jihar Ogun

    Gwamnatin jihar ogun da ke kudu maso yammacin Najeriya ta ce mutum 105 cikin 108 da aka yi wa gwajin cutar korona a wani kamfanin da ke jihar sun kamu da cutar.

    Kwamishin Lafiyar jihar, Dr. Tomi Coker, ne ya bayyana haka ranar Laraba.

    A daren ranar Laraba, hukumar yaki da cutuka masu yaduwa ta kasar, NCDC, ta ce mutum hudu ne suka kamu da cutar a jihar, inda a jumlace mutum 475 suke dauke da korona a Ogun.

    Jihar tana makwabtaka da Lagos, inda cutar ta fi kamari a Najeriya.

    Tana cikin jihohin da shugaban kasar Muhammadu Buhari ya sanya wa dokar kulle a baya, ko da yake daga bisani an sassauta dokar.

  4. Sau 8 aka yi yunkurin yi wa Abacha juyin mulki - Al-Mustapha

    Tsohon babban dogarin marigayi janar Sani Abacha, Hamza Al-Mustapha, ya ce sau takwas ana yunkurin yi wa tsohon shugaban kasar juyin mulki.

    "Kafin lokacin da ya rasu, ana shirin yi masa juyin mulki na takwas ne amma 'yan Najeriya su suni cewa an yi masa yunkurin juyin mulki na uku ne amma gaskiyar magana ita ce guda takwas ne aka yi, a kan na takwas din ne ya rasu," in ji Al-Mustapha a hirarsa da BBC a dai-dai lokacin da marigayi Abacha ya cika shekara 22 da rasuwa.

    Al-Mustapha ya ce akwai gyara daga rahotannin da ake zargin cewa kudin da ake mayar da su Najeriya na tsohon shugaban ne. Ya ce wadannan kudade mallakar gwamnatin Najeriya da shugabannin al'ummar kasar su ka amince a ajiye su a asusun kasashen waje ne.

  5. Cutar korona ta kama mutum fiye da miliyan biyu a Amurka

    Mutanen da cutar korona ta kama a Amurka sun zarta miliyan biyu, a cewar jami’ar Johns Hopkins University da ke bin diddigin yaduwar cutar a duniya.

    Kamar yadda rahotanni suka nuna, Amurka ta kasance kasar da aka fi samun masu dauke da cutar korona saboda yawan gwajin da ake yi wa mutanen da ake zargi suna dauke da cutar.

  6. Buɗewa

      • Marubuci, Nasidi Adamu Yahya
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Hausa, Abuja

    Nasidi AdamuYahaya ne yake yi muku barka da wannan safiya.

    Muna fatan ku kasance tare da mu tsawon wannan rana domin sanin halin da duniya take ciki.

    Za mu kawo muku labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku, musamman kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da makwabtansu, har ma da sassan duniya.