Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Gwamnatin Sokoto ta rarraba takunkumin rufe fuska ga masallatai

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye kuma da dumi-duminsu game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya musamman masu alaka da annobar korona da ma karin wasu daban.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Kasuwar saye da musayar 'yan ƙwallon ƙafa, Makomar Coutinho da Willian da Haaland da Sancho da Pochettino da Kavertz

    Chelsea, Manchester United da kuma Leicester sun tuntubi wakilin dan wasan Barcelona Philippe Coutinho domin dauko shi a bazara, sai dai dan wasan na Brazil dan shekara 27 ya fi son komawa Chelsea.

    Dan wasan Chelsea mai shekara 31 na kasar Brazil, Willian ya nuna alamar zai iya sanya hannu a kan yarjejeniya ta takaitaccen lokaci zuwa karshen kakar wasa ta bana a yayin da ake sa ran kakar wasan Premier za ta zarta ranar 30 ga watan Yuni, wato ranar da kwangilarsa za ta kare.

    Tsohon dan wasan Liverpool John Barnes ya ce dan wasan Borussia Dortmund dan kasar Norway Erling Braut Haaland, mai shekara 19, yana da dukkan kwarewar da ta kamata wajen maye gurbin Roberto Firmino a Anfield.

  2. Muhimman abubuwan da suka faru a Najeriya a makon nan

    Tun daga ranar Lahadi, 17 ga watan Mayun 2020 zuwa ranar Asabar, abubuwa da dama muhimmai sun faru a Najeriya kuma sun ja hankulan 'yan kasar.

    Mun tsakuro muku muhimmai daga cikinsu:

    • Najeriya ta kama jirgin Birtaniya da ke 'jigilar fasinjoji'
    • Buhari ya bai wa sojoji umarnin kakkabe 'yan bindiga a Katsina
    • Saudiyya ta mayar da 'yan Najeriya kusan 300 gida
    • Coronavirus: An tsawaita dokar kulle a Kano da mako biyu
  3. Ba za a yi taron sallar Idi a Abuja ba

    Hukumomi a Abuja, babban birnin Najeriya, sun umarci mazauna garin musamman Musulmai da su gudanar da sallar Idi a gidajensu saboda yaƙin da ake yi da annobar korona.

    Wata sanarwa da Anthony Ogunleye, sakataren yaɗa labaran hukumar FCTA, ya fitar ranar Juma'a ta ce umarnin ya biyo bayan wanda fadar Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III ta yi ne cewa kowa ya yi sallah a gida da iyalinsa.

    Sanarwar ta ƙara da cewa: "Hakan ya biyo bayan umarnin da kwamitin shugaban ƙasa mai yaƙi da annobar korona ya bayar na cewa dukkanin wuraren ibada su ci gaba da kasancewa a rufe a Abuja da sauran wuraren da cutar ta yi ƙamari."

    Kazalika FCTA ta ce ta yi wata tattaunawa ta musamman da ƙungiyar limamai da kuma ta Kiristoci wato CAN a Abuja domin tabbatar da cewa an bi wannan umarni.

  4. Musulmai sun yi sallar Juma'a a coci saboda cikar masallacinsu a Jamus

    Wani coci a birnin Berlin na ƙasar Jamus ya buɗe ƙofofinsa ga ɗaruruwan Musulmai, waɗanda suka gaza shiga masallancinsu saboda dokar nesa-nesa da juna domin gudanar da sallar Juma'a a ƙarshen watan Ramadan.

    A farkon wannan wata ne aka ɗage matakan da aka sanya wa wuraren ibada a Jamus, sai dai masallacin Dar Assalam da ke babban birnin ƙasar na iya cin mutum 50 ne kawai a ƙarƙashin sabbin ƙa'idoji.

    Kan haka ne cocin St Martha da ke kusa ta yi tayin karɓar masallatan.

    Limamin masallacin Dar Assalam ya faɗa wa Reuters cewa: "Abin farin ciki ne musamman a irin wannan lokaci na annoba ga kuma watan Ramadan. Wannan annoba ta mayar da mu al'umma guda ɗaya."

    "Wannan baƙon abu ne saboda kaɗe-kaɗe da kuma hotuna," a cewar Samer Hamdoun, wani da ya yi sallah a cikin cocin.

    Mutum fiye da 179,710 ne suka kamu da korona a Jamus, inda 8,241suka mutu - abin da ya sa ta zama ta takwas a yawan masu cutar a duniya.

  5. Mutum fiye da dubu 330 sun kamu da korona a Brazil

    An sake samun gagarumar ƙaruwar mutanen da korona ta kama a ƙasar Brazil, inda adadin masu cutar ya zarce 330,000.

    Mutum sama da 21,000 ne kuma suka mutu. Amurka ce kadai ta samu yawan masu korona fiye da haka.

    Tun farko, Hukumar Lafiya ta Duniya ta ayyana Nahiyar Kudancin Amurka a matsayin wata sabuwar cibiyar annobar.

    Daraktan ayyukan ɗaukin gaggawa na hukumar ya ce ƙasashe da dama a yankin na ganin ƙaruwar tashin hankali ta mutanen da korona ke harba.

    Cutar ta yi wa ƙasashen Peru da Chile da Ecuador wawan kamu.

  6. Jama'armu na Nijar barkanku da Idin Ƙaramar Sallah

    Umar Mikail ke wa al'ummar Nijar da Senegal da Ivory Coast da saura barka da Idin Ƙaramar Sallah tare da fatan Allah ya maimaita mana - ku kuma 'yan Najeriya Allah ya kai mu gobe Lahadi ku ci naku tuwon sallar.

    Kazalika barkanku da shigowa shafinmu mai kawo rahotanni kai-tsaye kan abubuwan da ke faruwa a duniya musamman game da annobar cutar korona.

    Ku biyo mu.