Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Gwamnatin Sokoto ta rarraba takunkumin rufe fuska ga masallatai

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye kuma da dumi-duminsu game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya musamman masu alaka da annobar korona da ma karin wasu daban.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a daidai wannan lokaci muka kawo karshen kawo muku labarai da rahotanni kai-tsaye, sai kuma gobe idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Ga wasu daga cikin kanun labaran da muka wallafa a wannan shafin:

    • Mutum fiye da dubu 330 sun kamu da korona a Brazil
    • Sojoji sun 'kashe 'yan fashi 135' a Katsina da Zamfara
    • Za a buɗe wuraren ibada a Iran ranar Lahadi
    • Akwai yiwuwar ci gaba da gasar La Liga ranar 8 ga Yuni
    • Sifaniya za ta buɗe ƙasar ga masu yawan buɗe ido
    • An yi wa mutum miliyan 1.4 gwajin korona a rana guda a Wuhan
    • 'Ana neman waɗanda suka ce sun ga wata'
    • El-Rufai ya kai samame kan iyakar Kaduna da Kano
    • Yawan mace-mace na ƙara raguwa a Italiya
    • Iran za ta buɗe wuraren ibada ranar Lahadi
    • Covid-19: An sallami ƙarin mutum 45 a Legas
    • Gwamnatin Sokoto ta rarraba takunkumin rufe fuska ga masallatai

    Ku duba kasa domin karanta labaran da wasu muhimmai...

  2. Gwamnatin Sokoto ta rarraba takunkumin rufe fuska ga masallatai

    A yunƙurinta na daƙile yaduwar cutar korona, gwamnatin jihar Sokoto ta rarraba takunkumin rufe fuska ga masallatan Juma'a a fadin jihar saboda shirin Sallar Idi.

    Ma'aikatar lafiya ta jihar ce ta wallafa hakan a shafinta na Twitter inda ta ambato kwamishinan lafiya na jihar Dakta Muhammad Ali Inname yana cewa "gwamnatin jihar ta sayi takunkumin mai yawa domin raba wa jama'a kyauta."

    Kwamishinan lafiya na jihar ya bayyana cewa saka takunkumin rufe fuska ya zama wajibi a jihohin da ba a tsaurara dokar kulle ba.

  3. 'Yan Taliban sun tsagaita wuta saboda bikin ƙaramar sallah

    'Yan kungiyar Taliban a Afghanistan sun bayyana cewa za su tsagaita wuta na kwanaki uku saboda bikin ƙaramar sallah da za a yi a ƙasar.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ƙungiyar ke ƙara yawaita kai hare-hare ga dakarun gwamnatin Afghanistan a 'yan kwanakin nan duk da yarjejeniyar da ƙungiyar ta cimma da Amurka a watan Fabrairu.

    Ƙungiyar dai ta bayyana cewa ba za ta kai wani hari ba a cikin wa'adin da ta bayar na tsagaita wuta - sai dai sun ce za su kare kansu idan an kai musu farmaki.

  4. Covid-19: An sallami ƙarin mutum 45 a Legas

    Jihar Legas ta sallami ƙarin mutum 45 da suka warke bayan sun kamu da cutar korona.

    Gwamnatin jihar ce ta sanar da hakan a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na Twitter inda ta bayyana cewa a halin yanzu jumullar waɗanda suka warke daga cutar a jihar sun kai 707.

    Jihar Legas ce dai kan gaba a yawan masu cutar ta korona a Najeriya.

  5. An samu raguwar safarar miyagun ƙwayoyi a Mexico

    Gwamnatin ƙasar Mexico ta tabbatar da cewa an samu raguwar safarar miyagun ƙwayoyi da kusan kashi 25 cikin 100 tun bayan saka dokokin kulle saboda cutar korona

    Ta bayyana cewa yawan siya da siyarwar miyagun ƙwayoyin ya ragu ne sakamakon wuraren da ake siyar da su irin su gidajen siyar da barasa da kuma na sayar da abinci duk a kulle suke.

    Sai dai gwamnatin ta bayyana cewa an samu ƙaruwar rahotanni kan kisa a ƙasar kuma kisan na da alaƙa ne da gungun masu safarar ƙwayoyi.

    Sai dai a binciken da aka yi, ana ganin cewa gungun masu safarar ƙwayoyi ne daban-daban ke amfani da wannan lokaci wajen kai wa juna hari domin kece raini.

  6. Iran za ta buɗe wuraren ibada ranar Lahadi

    Shugaban ƙasar Iran Hassan Rouhani, ya bayyana cewa ƙasar za ta buɗe wuraren ibada da na tarihi a gobe Lahadi.

    Wannan na daga cikin 'yunƙurin ƙasar na sassauta dokar kulle domin ba jama'a damar yin murnar ƙaramar sallah.

    Mista Rouhani ya buƙaci masu kai ziyara wuraren tarihi da masu zuwa wuraren ibada da su guji yin cunkoso tare da bayar da tazara a tsakani.

    Iran ta bayyana cewa sama da mutum 7,000 a ƙasar sun mutu sakamakon cutar korona, sai dai a wani bangaren ana ganin kamar yawan mutanen sun ɗara haka yawa.

  7. Yawan mace-mace na ƙara raguwa a Italiya

    Yawan mutanen da suke mutuwa a ƙasar Italiya na ƙara raguwa a duk rana inda a yau aka samu mutum 119 da suka mutu.

    A jiya dai mutum 130 ne suka mutu wanda hakan ke nufin an samu raguwa da mutum 11.

    Kwanakin baya sai da sama da mutum 900 suka mutu a rana guda a ƙasar.

    A halin yanzu waɗanda suka mutu sakamakon cutar a ƙasar sun kai 32,735.

    Italiya ita ce ƙasa ta uku a yawan mutuwa sakamakon cutar korona bayan Amurka da Birtaniya.

  8. Mario Gotze zai bar Borussia Dortmund idan an kammala kakar 2019-20

    Mario Gotze zai bar Borussia Dortmund idan an kammala kakar bana, in ji daraktan wasannin kungiyar Michael Zorc.

    Mario mai shekara 27 ya buga wasa 201 a kaka biyu da ya yi a kungiyar, sai dai kuma karawa biyar ya yi wa Dortmund a kakar shekarar nan.

    Gotze ya lashe kofin Bundesliga biyar, kuma shi ne ya ci wa Jamus kwallo a wasan karshe da ta lashe kofin duniya a 2014.

  9. El-Rufai ya kai samame kan iyakar Kaduna da Kano

    Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai ya kai samame kan iyakar Kaduna da Kano domin tabbatar da hana zirga-zirga tsakanin jihohin biyu.

    A ranar Talata ne dai yayin wata hira da gwamnan ya sha alwashin zuwa kan iyakar jihohin biyu domin tabbatar da babu wanda ya keta dokar da aka saka.

  10. Waɗanda korona ta kashe a Birtaniya sun kai 36,675

    Ƙarin mutum 282 da suka kamu da cutar korona a Birtaniya sun sake mutuwa.

    A halin yanzu waɗanda suka mutu sakamakon cutar a Birtaniya sun kai 36,675.

    Sakataren sufuri na kasar Grant Shapps ne ya sanar da alƙaluman inda ya bayyana cewa "wannan ba wai alƙaluma bane kaɗai amma tunatarwa ga yadda wannan cuta ta yi tsanani".

  11. Yadda Shugaban Nijar ya yi Sallar Idi a yau Asabar

  12. 'Ana neman waɗanda suka ce sun ga wata'

    Kwamitin duba wata na Fadar Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III ya ce yana neman agajin mutane da su taimaka masa wurin neman duk wanda ya ce ya ga watan Shawwal a daren Juma'a.

    Shugaban kwamitin, Farfesa Usman el-Nafaty ne ya tabbatar wa BBC hakan, inda ya ce suna neman mutanen ne domin tattaunawa da su da nufin tabbatar da sahihancin abin da suka gani.

    Tun farko wani shafin Facebook ne mai ɗauke da sunan kwamitin ganin watan ya wallafa sanarwar cewa ana neman mutanen.

    "Muna roƙo idan kuna cikin waɗanda suka ga watan Shawwal na shekarar 1441 a kowanne lungu da saƙo na Najeriya ranar Juma'a, ko kuma kun san wanda ya gani, ko kun san yadda za a cimma wanda ya gani to ku bayyana mana a nan," in ji sanarwar.

    Ta ƙara da cewa: "Mambobin kwamitin ganin wata na son su tattauna da mutanen game da batun domin su taimaka musu (kwamitin) wurin aiwatar da aikinsu a matsayinsu na masu bai wa Mai Alfarma Sarkin Musulmi shawara."

    A daren Juma'a ne dai kwamitin ya bayar da sanarwar cewa ba a samu rahoton ganin wata ba, saboda haka za a cika azumi 30, inda za a yi sallar Idi ranar Lahadi.

  13. An yi wa mutum miliyan 1.4 gwajin korona a rana guda a Wuhan

    An yi gwajin cutar korona ga mutum 1,470,950 a ranar Juma'a a garin Wuhan kamar yadda ma'aikatan lafiya suka bayyana.

    A farkon watan nan ne dai mahukunta a garin suka ce suna sa rai za su yi gwaji ga mutum miliyan 11 a ƙasa da makonni biyu.

    An tsara yin wannan gwajin ne domin gano wadanda suke dauke da cutar amma ba su nuna alamunta a tattare da su ba.

    Sun bayyana cewa suna ganin wannan ce hanya kaɗai da za a iya ci gaba da kasuwanci da kuma buɗe makarantu a garin.

  14. Sifaniya za ta buɗe ƙasar ga masu yawan buɗe ido

    Ƙasar Sifaniya za ta buɗe kofa ga masu yawan buɗe ido daga ƙasashen duniya domin ci gaba da shiga ƙasar.

    Firai Ministan ƙasar Pedro Sánchez ne ya bayyana hakan a wata sanarwa inda ya ce za a buɗe ƙasar ne daga watan Yuli.

    Sai dai bai bayar da takamaimai rana ko kuma ƙarin bayani ba kan matakai da za a dauka kafin buɗe ƙasar.

    Mista Sánchez ya kuma bayyana cewa akwai yiwuwar ci gaba da gasar La Liga a farkon watan Yuni.

    Ƙasar Sifaniya na daya daga cikin ƙasashen da cutar korona ta yi wa mummanan kamu inda aka samu mace-mace da dama.

  15. Labarai da dumi-dumi, Akwai yiwuwar ci gaba da gasar La Liga ranar 8 ga Yuni

    Gwamnatin Spaniya ta sanar da cewa za a iya ci gaba da gasar La Liga daga ranar 8 ga watan Yuni.

    An dakatar da La Liga saboda annobar korona tun a watan Maris amma 'yan wasa sun koma atasaye a farkon watan nan da fatan ci gaba da wasannin ba tare da 'yan kallo ba.

    Spaniya na cikin ƙasashen da suka fi fama da annobar kuma a 'yan makonnin nan ne ta sassauta dokar kulle.

    Mutum 234,824 ne suka harbu da cutar korona a Spaniya, a cewar alƙaluman Jami'ar Johns Hopkins, inda 28,628 suka mutu.

  16. Za a buɗe wuraren ibada a Iran ranar Lahadi

    Shugaban Iran, Hassan Rouhani, ya sanar cewa za a buɗe wuraren ibada da na al'adu ranar Lahadi, yayin da ƙasar ke sassauta dokar kulle domin daƙille annobar korona.

    Wannan yana zuwa ne yayin da ake shirin gudanar da bikin Ƙaramar Sallah bayan kammala azumin Ramadan.

    Rouhani ya shawarci masu ziyara a ƙaburburan shehunai da kada su yi cunkoso sannan su yi nesa-nesa da juna.

    A mako mai zuwa ne ake sa ran sanar da matakan da za a bi wurin dawo da harkoki a ƙasar.

    Iran ta ce fiye da mutum 7,000 ne suka mutu sakamakon cutar korona, amma ana ganin adadin ya fi haka.

  17. Sojoji sun 'kashe 'yan fashi 135' a Katsina da Zamfara

    Dakarun rundunar Hadarin Daji ta sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe 'yan fashi 135 a wani hari ta sama a jihohin Kastina da Zamfara cikin kwana biyu.

    A wata sanarwa da jami'in tattara bayanai na hedikwatar tsaro da ke Abuja, Manjo Janar John Enenche, ya fitar ranar Asabar ta ce an kai hare-haren ne a ranakun Laraba 20 ga watan Mayu zuwa Juma'a 22, inda ta lalata sansanoninsu.

    Daga cikin sansanonin da aka hara akwai Sansanin Abu Radde na ɗaya da na biyu, da kuma Dunya da ke ƙananan hukumomin Jibya da Ɗan Musa dukansu a Jihar Katsina, a cewar rundunar.

    Sauran sun haɗa da Sansanin Hassan Tagwaye da Sansanin Maikomi da ke ƙananan hukumomin Birnin Magaji da kuma Zurmi na Jihar Zamfara.

  18. Lafiya Zinariya: Yadda cutar jijjiga ke lalata jijiyoyin jikin mace

    Zama ko girman mabiyiya a jikin mace mai ciki na da alaka da cutar jijjiga da wasu mata ke samu a yayin da suke da juna biyu.

    Dr. Maryam Sulaiman ta asibitin Abdullahi Wase da ke Jihar Kano ta yi wa Habiba Adamu bayani game da cutar ta jijjiga da ke damun mata masu ciki musamman a arewacin Najeriya.

  19. Girman taɓarɓarewar tattalin arzikin China

    Duk da yake masana tattalin arziƙi na iƙirarin cewa bayanai da suka shafi tattalin arziƙin China ba abu ne da ya kamata a gasgata ba, yanzu suna cikin ruɗani - ana ganin babu wasu alƙaluma ma kwata-kwata a halin yanzu.

    A ranar Juma'a, China ta bayyana cewa a wannan shekarar ba za ta ƙayyade wani mataki da take son kai wa ba wajen haɓaka tattalin arziƙin ƙasar saɓanin yadda ta saba yi a baya.

    Wannan wani abu ne da ƙasar ba ta taɓa yi ba tun bayan fara wallafa muradan da take son cimmawa duk shekara tun daga 1990.

  20. Trump ya ci alwashin buɗe wuraren ibada ko gwamnoni ba sa so

    Shugaba Donald Trump na Amurka ya yi kira ga gwamnoni da su buɗe wuraren ibada, waɗanda yanzu haka suke a rufe saboda tsoron yaɗuwar korona, yana mai cewa masallatai da coc-coci "wurare ne masu muhimmanci".

    "Wasu gwamnonin sun ce shagunan shan barasa suna cikin abubuwa masu muhimmanci amma sun ce ban da wuraren ibada, wannan ba daidai ba ne," in ji Trump.

    Ya ƙara da cewa: "Yawan addu'o'i muke buƙata a Amurka ba ƙarancinsu ba."

    Kazalika ya ci alwashin cewa zai buɗe su da kansa ko ba da son gwamnonin ba.

    Shugaban ba shi da ikon yin hakan a doka, sai dai zai iya janye tallafin gwamnatin tarayya zuwa jihohin.