Wasu daga cikin 'yan Najeriya da aka kwaso daga Dubai na da korona
Kwamishinan Lafiya na Jihar Legas Farfesa Akin Abayomi ya bayyana a yau Lahadi cewa gwaji ya nuna uku daga cikin 'yan Najeriya da aka ɗebo daga ƙasar Daular Larabawa ko kuma Dubai sun kamu da cutar korona.
Kwamishinan ya ƙara da cewa tuni aka kai su cibiyoyin killace masu cutar domin ɗaukar mataki na gaba.
Kazalika ya jaddada cewa Legas za ta ci gaba da ɗabbaƙa dokokin killacewa domin daƙile cutar - Legas ce cibiyar cutar korona a Najeriya da mutum 2,373 da suka kamu da ita.
Ministan Harkokin Wajen Najeriya ya ce za a riƙa killace 'yan ƙasar da aka kwaso zuwa gida daga ƙasashen waje na tsawon mako biyu a Abuja.
Wasu daga cikin ƙasashen da aka kwaso 'yan Najeriya sun haɗa da Birtaniya da Amurka da Dubai.