Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Mai cutar korona ta haihu a Legas

Wannan shafi na kawo muku bayanai da rahotanni kai tsaye kuma da dumi-duminsu dangane da annobar korona da ma wasu karin batutuwa da ke wakana a fadin duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail, Mustapha Musa Kaita and Awwal Ahmad Janyau

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a daidai wannan lokaci muka kawo karshen kawo muku labarai da rahotanni kai-tsaye, sai kuma gobe idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Ga wasu daga cikin kanun labaran da muka wallafa a wannan shafin:

    • Fiye da miliyan huɗu da rabi sun kamu da korona a duniya
    • An saka ranar dawo da tafiye-tafiye a Italiya
    • An kashe 'yan fashi 27 a Zamfara
    • Korona ta hana marasa lafiya miliyan 2 zuwa asibiti a Najeriya
    • NNPC ya bai wa Abuja kyautar asibiti don kula da masu korona
    • Ana murnar rabuwa da Ebola sai ga kuma korona
    • Jaririya 'yar wata huɗu ta kamu da korona a Kaduna
    • Mutum na ƙarshe mai Ebola ya gudu a Congo
    • Buhari ya karbi maganin korona na Madagascar
    • Mutum 55 sun sake warkewa daga korona a Jigawa

    Ku duba kasa domin karanta labaran. Mu kwana lafiya....

  2. 'Kungiyar IS na kokarin farfadowa'

    Sabon Firai Ministan Iraki Mustafa al-Kadhimi ya yi gargadin cewa kungiyar IS na kokarin farfadowa bayan wasu hare-hare da kungiyar ta kai.

    Hukumomi a kasar Iraki sun bayyana cewa a makonnin da suka gabata, a kalla kungiyar ta kai hare-hare 17 ga fararen hula da jami'an tsaro a yankuna hudu na kasar.

    Kungiyar dai ta fito da wani sabon bidiyo mai tsawon mintuna 50 da ke nuna yadda kungiyar ke cin karenta ba babbaka ta hanyar kai hare-hare irin na kunar baƙin wake da kwantar bauna da sauransu.

    A 2017 ne dai aka ci galba kan kungiyar IS inda aka gurgunta ta, amma a halin yanzu ta dawo da kai hare-hare.

  3. Mutum 4 sun sake warkewa daga korona a Sokoto

    Jihar Sokoto ta sake sallamar mutum hudu wadanda suka warke daga cutar korona a jihar.

    Ma'aikatar kiwon lafiya ta jihar ce ta sanar da hakan a shafinta na Twitter inda ta ce an sallami marasa lafiyar ne daga wurin killace masu dauke da cutar na Amanawa da ke jihar.

    A halin yanzu mutum 61 ne jumullar wadanda suka warke daga cutar a jihar kamar yadda ma'aikatar lafiya ta jihar ta sanar.

    Mutum 13 ne suka mutu sakamakon cutar sa'annan 112 suka kamu da ita a jihar ta Sokoto kamar yadda kididdigar hukumar NCDC ta nuna a ranar Juma'a.

  4. Labarai da dumi-dumi, Mai cutar korona ta haihu a Legas

    Wata mata mai dauke da cutar korona ta haihu a wurin killace masu cutar a Legas.

    Gwamnatin jihar Legas ta tabbatar da hakan a shafinta na Twitter inda ta ce matar ta haihu ne a wurin killace masu cutar na Gbagada, wanda daya ne daga cikin wuraren da ake kula da masu cutar a jihar.

    Wannan ne karo na farko da mai dauke da wannan cuta ta haihu a Najeriya tun bayan bullar cutar.

    Sai dai babu wani cikakken bayani dangane da ko jaririn na dauke da wannan cuta ta coronavirus.

  5. An nada sabon ministan lafiya a Brazil

    Shugaban Brazil Jair Bolsonaro ya nada Janar Eduardo Pazuello a matsayin ministan lafiya na wucin gadi a kasar bayan murabus din da Nelson Teich ya yi a makon nan.

    Sai dai Mista Pazuello ba kwararre bane a bangaren kiwon lafiya domin ya shafe kusan shekarunsa na aikin soja a bangaren kula da makamai da kayayyakin sojoji na kasar.

    A wannan makon ne Mista Nelson ya yi murabus daga mukamin ministan lafiya na Brazil bayan ya samu rashin jituwa tsakaninsa da Shugaban Brazil Jair Bolsonaro dangane da yadda yake tafiyar da annobar korona a kasar.

  6. Daruruwan mutane na zanga-zanga kan dokar kulle a Landan

    Daruruwan jama'a ne dai ke ci gaba da yin zanga-zanga a Landan kan dokar kulle da aka kakaba a Ingila.

    'Yan sandan kasar sun bayyana cewa tuni aka kama mutum shida cikin masu zanga-zangar.

    Cikin wadanda aka kama har da Piers Corbyn, dan uwa ga Jeremy Corbyn wanda shi ne tsohon shugaban jam'iyyar Labour a Birtaniya.

    Masu zanga-zangar sun bayyana cewa an take hakkinsu na magana da kuma walwala sakamakon irin dokokin da aka kakaba musu kan coronavirus.

  7. Fiye da mutum 52,000 suka kamu da korona a Saudiyya

    Yawan waɗanda suka kamu da cutar korona a Saudiyya sun zarta dubu hamsin.

    Ma'aikatar lafiya ta Saudiyya ta ce cikin sa'a 12 kusan mutum 3,000 suka kamu da korona.

    Yawan wadanda cutar ta kashe kuma sun kai 302.

    Saudiyya dai ta kafa dokar hana fita a kasar, yayin da ya rage mako daya al'ummar musulmi su gudanar da bikin Sallah.

  8. Yadda aka fara duba marasa lafiya ta waya a Kano

    Wata Kungiya a jihar Kano ta kirkiri hanyar tattaunawa da likita ta waya da nufin rage dawainiyar zuwa asibiti da kuma haduwa da jami`an kiwon lafiya kai-tsaye, tare da kauce wa sauran hadura, musamman annobar korona.

    Kungiyar Covid 19 Relief Alliance ce ta kirkiri wannan tsarin, inda tuni wasu kungiyoyi suka fara hada gwiwa da likitoci a Asibitin koyar wa na Mallam Aminu Kano da ke Kano da wasu asibitocin don fara duba marasa lafiya daga gida.

  9. Mutum 55 sun sake warkewa daga korona a Jigawa

    Gwamnatin Jigawa ta tabbatar da warkewar mutum 55 daga cutar korona wadanda ta ce tuni aka salleme su.

    A shafinta na Twitter, gwamnatin jihar ta ce a halin yanzu jumullar wadanda aka sallama sakamakon cutar sun kai 62 inda kuma cutar ta kashe mutum uku a jihar.

    A kididdigar hukumar da ke yaki da cutuka masu yaduwa ta Najeriya NCDC a daren Juma'a, jumullar mutum 191 ne suka kamu da cutar a jihar ta Jigawa.

  10. Labarai da dumi-dumi, Buhari ya karbi maganin korona na Madagascar

    A yau Asabar ne Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya karbi maganin gargajiya na Madagascar wanda ake ikirarin yana magance cutar korona da ta addabi duniya.

    Shugaban kasar Guinea Bissau Umaro Sissoco Embaló ne ya zo da maganin inda ya bai wa shugaba Buhari.

    Sai dai Buhari ya tabbatar da cewa ba zai bari a yi amfani da maganin ba har sai masana kimiyya sun tabbatar da kuma tantance ingancin maganin.

  11. Mutum na ƙarshe mai Ebola ya gudu a Congo

    Hukumomin lafiya a Jamhuriyyar Dikokuradiyyar Congo sun ce mutum ɗaya da ya rage a cibiyar killace masu cutar Ebola ya gudu bayan tabbatar da yana ɗauke da cutar.

    An bayyana cewa ya gudu ne a ranar Asabar bayan gwaji ya tabbatar da yana ɗauke da Ebola.

    Hukumomi sun ce babu wani cikakken bayani game da mutumin da suka ce mai shekaru 28 daga yankin Beni na gabashin Jamhuriyyar Dimokuradiyyar congo.

    Ma'aikatar lafiya ta ce duk wani yunƙuri na gano inda ya yake ya cutura zuwa yanzu.

    Ebola ta sake ɓarkewa a Congo karo na 10 tun 10 ga Afrilu, kuma saura kwana biyu a sanar da kawo ƙarshen cutar, aka sake samun mutum bakwai da suka kamu yayin da 4 suka mutu.

    Yanzu Congo na fama ne da yaƙi da Ebola da kuma cutar korona annoba a duniya.

  12. Buhari ya karbi bakuncin shugaban Guinea Bissau

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya karbi bakuncin Shugaban kasar Guinea Bissau Umaro Sissoco Embaló a ranar Asabar a Abuja.

  13. Kenya ta rufe iyakokinta da Somalia da Tanzania

    Shugaban Kenya, Uhuru Kenyatta ya bayar da umarnin rufe iyakokin ƙasar tsakaninta da ƙasashen Tanzania da Somalia daga daren Asabar, ban da masu jigilar dakon kaya.

    Dirobobin manyan motoci ne kaɗai da aka tabbatar ba sa ɗauke da cutar korona za a bari su wuce. Shugaban ya faɗa a makon da ya gabata cewa gwaji ya nuna direbobi 78 na ɗauke da cutar a kan iyakokin ƙasar kuma an hana su shiga.

    Kazalika shugaban ya tsawaita dokar hana fita da ke aiki tsakanin maraice zuwa asuba har zuwa 6 ga watan Yuni. Haka ma zirga-zirga tsakanin birane biyar ciki har da birnin Nairobi an tsawaita ta.

    Kenyatta ya ce Kenya na da mutum 481 da ke ɗauke da cutar korona a yanzu haka da kuma 50 da suka mutu - hakan na nufin ƙarin mutum biyar sun mutu a cikin sa'a 24 da suka wuce.

  14. Gwamnatin Najeriya ta yi gargaɗi ga waɗanda suka warke daga korona

    Gwamnatin Najeriya ta yi gargaɗi ga mutanen da suka warke daga cutar korona su daina bayar da cikakkun bayanai kan magungunan da suka warkar da su, don kada mutane su dinga yin gaban kansu.

    Sakataren gwamnatin Tarayya kuma shugaban kwamitin shugaban kasa na yaƙi da cutar korona Boss Mustapha ne ya bayyana haka a taron manema labarai game da halin da ake ciki kan matakan da gwamnati ke ɗauka na daƙile cutar a Najeriya.

    Ya ce wasu da suka warke kuma aka sallame su, sun fito suna bayyana irin magungunan da aka ba su wanda a cewarsa zai sa waɗanda ke fama da cutar korona su dinga saye suna sha ba tare da shawarar likita ba.

    Ya ƙara yin kira ga duk wanda ya ji alamomin cutar korona ya yi gwaji, ko ya kai kansa ɗaya daga cikin cibiyoyin killace masu dauke da cutar korona domin samun kula ta musamman.

    Ya ce magance alamomin cutar ya sha bamban da magance cutar baki ɗaya, don haka suke yin kira a guje wa shan magani ba tare da shawarar likita ba.

  15. Labarai da dumi-dumi, Jaririya 'yar wata huɗu ta kamu da korona a Kaduna

    Gwamnatin Jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya ta tabbatar da cewa an samu jaririya 'yar wata huɗu a cikin ƙarin mutum 20 da suka kamu da cutar korona ranar Juma'a.

    Ma'aikatar lafiya a jihar ta ce bincikenta ya nuna cewa mahaifin jaririyar ya je jihar Kano a 'yan kwanakin nan.

    Ta ƙara da cewa an yi wa jaririyar gwajin cutar ne bayan an kai ta asibiti bisa matsalar numfashi kuma yanzu haka ana jiran sakamakon gwajin da aka yi wa iyayenta.

    Kazalika akwai ma'aikatan lafiya shida a cikin sabbin waɗanda suka harbu da cutar. Guda 15 daga cikin 20 ɗin 'yan uwan wani mai ɗauke da cutar ne, a cewar ma'aikatar lafiyar jihar a wata sanarwa da ta wallafa a Twitter ranar Asabar.

    Sanarwar da Kwamishinar Lafiya Amina Mohammed-Baloni ta sanya wa hannu ta ce yanzu cutar korona ta ɓulla a ƙananan hukumomi tara na jihar Kaduna.

    Hukumar NCDC ta ce mutum 134 ne suka kamu da cutar korona a Kaduna ya zuwa daren Juma'a.

  16. Ana murnar rabuwa da Ebola sai ga kuma korona

    Wasu ma'aikatan lafiya a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo sun ɓarke da sowa bayan an sallami maras lafiya na ƙarshe da ke fama da cutar Ebola a ƙasar.

    Wannan ci gaba na zuwa ne yayin da ake fafata wani yaƙin da annobar cutar korona a ƙasar, wadda tuni ta yi sanadiyyar rasa ran mutum 61 tare da kama 1,370, a cewar aƙaluman Jami'ar Johns Hopkins.

    Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) reshen Afirka ta ce an sallami maras lafiyar ne a garin Beni, gari na ƙarshe da Ebola ta fi yin ƙamari.

    Sai dai hukumar ta ce jami'anta za su ci gaba da kasancewa a ƙasar domin sa ido na tsawon kwana 42.

    Ana saura kwana biyu kacal a bayyana ƙasar a matsayin wadda babu Ebola a cikinta sai aka gano wasu mutum biyu ɗauke da cutar a watan Afrilu.

    A ƙa'idar WHO sai an yi kwana 42 ba tare da samun wani sabon mai ɗauke da cutar ba sannan za a bayyana cewa ƙasar ta kawo ƙarshen cutar.

  17. NNPC ya bai wa Abuja kyautar asibiti don kula da masu korona

    A jiya Juma'a ne shugaban kamfanin mai na Najeriya NNPC, Mele Kyari ya bayar da gudummar asibiti ga hukumomin birnin Abuja - Babban Birnin Tarayyar Najeriya - mai cin gado 70 a madadin kamfanin.

    Ministan Abuja Malam Mohammed Musa Bello wanda ya jagoranci tawagar hukumar birnin (FCTA) zuwa wurin taron, ya gode wa kamfanin NNPC bisa ayyukan ci gaba da ya saba kawo wa birnin.

    "Ina godiya ga NNPC da kuma ɗaukacin ma'aikatar mai da iskar gas dangane da tallafin da suke bai wa Abuja a yaƙi da annobar korona da kuma rawar da NNPC ke takawa a ci gaban birnin Abuja na tsawon shekaru," in ji ministan a wani saƙon Twitter.

    Ya zuwa daren Juma'a, jumillar mutum 386 ne suka harbu da cutar korona a Abuja, yayin da bakwai suka rasa rayukansu da kuma 88 da suka warke.

  18. Korona ta hana marasa lafiya miliyan 2 zuwa asibiti a Najeriya

    Ministan Lafiya na Najeriya ya ce kimanain kashi 50 cikin 100 na marasa lafiya masu zuwa asibitoci a duba su sun daina zuwa asibitocin.

    Dr Osagie Ehanire ya ce adadin mata masu juna biyu da ke zuwa asibiti da kuma ayyukan riga-kafi sun ragu matuƙa, tun daga lokacin da aka samu bullar cutar korona a kasar.

    Dr Ehanire wanda ya yi bayani a wurin taron manema labarai na kullum da kwmaitin yaƙi da cutar korona na ƙasa ke yi a Abuja, ya ce adadin marasa lafiya da ke zuwa asibitoci a matakin je-ka-ka-dawo, wato wadanda ba a kwantar da su ba, ya ragu daga mutum miliyan hudu zuwa miliyan biyu a duk rana.

  19. An kashe 'yan fashi 27 a Zamfara

    Hedikwatar rundunar sojojin Najeriya da ke Abuja, babban birnin ƙasar ta ce ta halaka 'yan fashi 27 a kan iyakar jihohin Zamfara da Katsina.

    A samamen da rundunar tsaro ta musamman mai laƙabin Hadarin Daji ta kai wa 'yan fashin ranar Alhamis, an kashe su tare da lalata wasu daga cikin sansanoninsu bayan samun wasu bayanan sirri, kamar yadda rundunar ta bayyana a wata sanarwa a shafinta na Twitter.

    Rundunar ta ƙara da cewa bayan samun rahotannin sirrin ne kuma ta bazama, inda jiragenta mai saukar ungulu da kuma mai kai hari ta sama suka isa matsuguninsu da ke haɗakar garuruwan Nahuta da kuma Doumborou.

    A baya-bayan nan sojoji na bayyana irin nasarar da suke samu a kan masu ɗauke da makamai, sai dai babu wata kafa mai zaman kanta da ke tabbatar da nasarorin.

    Gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Muhamnmadu ta ce tana bakin ƙoƙarinta amma ko a ranar 20 ga watan Afirlu an samu rahoton mutum 47 da 'yan bindiga suka kashe a Katsina.

    Yankin jihohin Zamfara da Katsina da Sokoto suna fama da hare-haren 'yan fashi a baya-bayan nan kuma hakan ya haddasa rasa rayuka da dama tare da raba wasu da mahallansu.

  20. Kun tuna cewa WHO za ta fara darussa kan korona da Hausa?

    A jiya Juma'a muka kawo muku rahoton cewa Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) za ta fara koyar da darussan wayar da kai game da annobar korona da harshen Hausa - na san za ku tuna.

    To yanzu mun ji ta bakin masana harkar lafiya kan ko me hakan ke nufi.

    Latsa hoton da ke ƙasa domin jin abin da Dr Sani Gwarzo ya shaida wa BBC.