An bude masallatai da coci-coci a jamhuriyar Nijar
Za a bude masallatai da coci-coci a jamhuriyar Nijar bayan sassauta dokar kunle da za ta bai wa Musulmi da Kiristoci samun zarafin gudanar da ibadunsu daga yau Laraba.
Gwamnatin Nijar din dai ta ce ta dauki wannan matakin ne bayan gano cewa al'amura sun fara daidaita dangane da bazuwar cutar ta korona.
To sai dai gwamnatin ta ce dole ne a feshin kashe cututtuka a masallatan da coci-coci kafin masu ibada su fara amfani da wuraren.
To sai dai gwamnatin ta ce otal-otal da filayen jirgin sama da iyakokin kasar za su ci gaba da kasancewa a rufe.
Jmahuriyar Nijar dai na da mutum 854 da ke dauke da cutar korona, inda mutum 47 suka mutu.