Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Ma'aikatan lafiya 14 sun kamu da cutar korona a Katsina

Wannan shafi yana kawo muku bayanai kai tsaye dangane da annobar korona da ke ci gaba da yi wa duniya fyadar 'ya'yan kadanya.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Awwal Ahmad Janyau and Nasidi Adamu Yahaya

  1. Cutar korona ka iya ajalin Amurkawa 100,000 - Trump

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya yi gargadin cewa akwia yiwuwar samun mutum 100,000 da za su mutu sakamakon cutar korona.

    Mista Trump ya fadi hakan ne a lokacin da yake wani jawabi inda ya kuma musanta cewa gwamnatinsa na jan kafa wajen yakar cutar.

    Fiye da mutum 67,000 ne dai cutar korona ta yi ajali a Amurka.

    To saidai Mista Trump ya bayyana irin karfin gwiwar da yake da hsi dangane da samun rigakafin cutar a cikin watanni 12 ko 18.

  2. Gwamna Tambuwal ya saka dokar hana zirga-zirga a Sokoto

    Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya ce jihar na fuskantar karuwar masu dauke da cutar korona inda ya zuwa ranar Lahadi adadin masu cutar a jihar ya kai 66 sannan kuma mutum 8 sun mutu.

    Saboda haka ne Gwamnan ya ce daga ranar Litinin din nan gwamnati ta saka dokar hana zirga-zirga daga karfe 8:00 na dare zuwa karfe 6:00 na safe.

    Wannan dai na dauke a cikin wani jawabi da ya yi wa 'yan jihar a ranar Lahadi domin sanar da su irin halin da jihar ke ciki dangane da annobar korona.

    Gwamna Tambuwal ya kuma nemi ‘yan jihar da su rungumi al’adar wanke hannaye da kuma yin nesa-nesa da juna

    Daga karshe gwamna Tambuwal ya yi kira ga gwamnatin Tarayya da ta kai wa jihar ta Sokoto dauki ta hanyar kayan aiki da manufar dakile yaduwar annobar.

  3. Za a samar da rigakafin cutar korona zuwa karshen shekara - Trump

    Shugaba Trump na Amurka ya ce yana da tabbacin zuwa karshen shekara za a samar da rigakafin cutar korona.

    Jami'an lafiya sun ce sun yi amanna cewa samar da rigakafin zai dau tsawon watanni akalla 12 zuwa 18.

    Mista Trump ya yi watsi da sukar da ake yi masa cewa gwamnatinsa na tafiyar hawainiya wajen daukan matakai, inda ya dage a kan cewa matakin da ya dauka na sanya dokar hana fita ya ceto rayuka.

    Shugaban ya ce yana fatan zaben shugabanci Amurka na watan Nuwamba mai zuwa zai kasance zaben raba gardama kan yadda ya tunkari barkewar annobar - saboda ya yi amanna cewa ya yi abin da ya dace.

  4. An bude birnin Abuja da Legas bayan makonni biyar a rufe

    A ranar Litinin umarni sassauta dokar hana fita ke soma aiki a babban birnin Tarayyar Najeriya wato Abuja, da cibiyar kasuwancin kasar Legas a wani mataki na takaita gurguncewar tattalin arzikin kasar mafi karfin a Afirka.

    Wannan sabon umarni na nufin za a bude shaguna da kasuwanni daga safe har zuwa 3 na rana, Sai dai haramcin gudanar da taro zai ci gaba da aiki,kuma babu batun bude makarantu da wuraren ibada..

    Wasu ma'aikata za su koma bakin aikinsu, sannan dokar hana zirga-zirga za ta yi aiki da daddare.

    Har wa yau, an sanya wajabci kan sanya takunkumi da kuma zama nesa-nesa da juna domin hana yaduwar cutar.

    Najeriya dai na cigaba da samun karuwar alkalumma mutane da ke kamuwa da cutar korona inda sabbin alkaluman hukumar dakile cutuka ta kasar ke cewa sama da mutum dubu biyu da dari biyar ne suka kamu da cutar.

  5. Kasashen Gabas ta Tsakiya sun sassauta dokar kulle

    Kasar Tunisia ta sassauta dokar kulle da ta kakaba na tsawon mako shida. Kusan rabin ma'aikatan gwamnati da kamfanoni za su koma bakin aikinsu, sannan amfani da takunkumi wato face mask zai zama wajibi.

    Masar za ta bai wa otel-otel damar budewa ga baki 'yan yawon bude ido tsakanin jihohin kasar, kan sharudan rage adadin mutane da suke karba da kashi 25 cikin 100.

    A Lebanon ma kantunan sayar da abinci da gyaran gashi za su bude, kuma mutane za su iya fita motsa jiki da shan iskar bakin teku.

    A Iran za a bude masallatai a birane da dama da ba a samu yaduwar cutar da yawa ba.

  6. Coronavirus: Wasu kasashen Turai na sassauta dokar kulle

    Kasahen Turai da dama na cigaba da daukan matakan sassauta dokar kulle.

    Daga cikinsu akwai Portugal da Spaniya da Croatia da Girka, inda za a bude kananan shaguna da shagon gyaran gashi a yau Litinin.

    Wasu makarantu za su bude a yau a Jamus da Austria, yayin da a Hungary da Serbia da Slovenia kantunan cin abinci da barasa za su soma aiki bisa sharudan wasu matakai.

    Poland kuma za ta bai wa Otel-Otel da manyan shagunan da wasu gidajen adana kayan tarihi damar sake budewa.

  7. Coronavirus; Donald Trump na ci gaba da zargin China

    Shugaba Trump ya soki China kan gazawa wajen dakile yaduwar cutar korona, inda ya zarge ta da rikon sakainar kashi da yin rufa-rufa.

    A wani taron da aka nuna kai tsaye a tashar talabiji, da niyyar sake kaddamar da yakin neman zabensa, Mista Trump ya ce China ta gaza bai wa kasashen duniya hadin-kai domin taimakama ta lokacin da cutar ke yaduwa a birnin Wuhan.

    Mista Trump ya ce ba zai kakabawa kasar haraji ba a matsayin martani, sai dai ya ce gwamnatinsa za ta gabatar da hujjoji da ke tabbatar da abin da yake kokarin shaida wa duniya.

    Danganta tsakanin kasashen biyu masu karfin tattalin arziki a duniya na sake sukurkucewa, inda Amurka ke zargin cewa asalin wannan annoba daga wata cibiyar gwaje-gwajen ne da ke birnin wuhan.

  8. Hakikanin abin da na ce kan mace-mace Kano - Dr Sani Gwarzo

    Kwamitin da shugaban Najeriya ya aike Kano domin shawo kan yaduwar annobar korona ya musanta rahotannin da ake yadawa a kansa kan mace-macen jihar.

    Tun a yammacin Lahadi wasu kafafan yadda labaran kasar ke cewa kwamitin ya danganta karuwar mace-macen jihar da korona.

    Sai dai shugaban kwamitin, Dr. Nasir Sanu Gwarzo ya shaida wa BBC cewa ba haka abin yake ba.

    Dr. Gwarzo ya ce da alama ba a fahimci bayanansa ba, domin shi maganar da yake ba ta da alaka da wadannan bayanai da ake yadawa.

    "Na yi maganar kashi 80 cikin 100 amma ba a kan mace-mace ba, na yi wannan maganar ne kan samfurin da aka karba da kuma yanayin tasirin cutar a jikin dan Adam".

  9. Ce-ce-ku-ce kan sassauta dokar kulle a Kano

    Masana harkokin lafiya da mutane daidaiku sun soma bayyana ra'ayoyinsu kan matakin da gwamnatin jihar Kano ta dauka kwatsam na sassauta dokar kulle duk da samun karuwa a yaduwar cutar korona a jihar.

    Ranar Asabar, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar ta Kano, ya sanar da sassauta dokar hana fitar wacce Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya saka ta tsawon kwana 14.

    Gwamnatin Kano ta ce mazauna birnin Kano za su iya fita a ranakun Litinin da Alhamis daga karfe 10:00 na safe zuwa 4:00 na yamma domin sayen abinci da magani.

    Sai dai gwamnan ya ce manyan kantunan sayayya ne kadai za su bude, yayin da kasuwanni za su ci gaba da kasancewa a rufe.

    Gwamnan ya dauki matakin sassauta dokar kullen ne a daidai lokacin da cutar koron ke ta'azzara a jihar ta Kano.

  10. Budewa

    Masu bibiyarmu barkan ku da war haka. Da fatan kuna cikin koshin lafiya. Yau ma mun dawo da shirinmu na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da abubuwan da ke faruwa kan annobar korona da ke addabar duniya. Da fatan za ku kasance da shafin bbchausa.com domin samun wadannan bayanai.