Rundunar tsaron Najeriya ta ce dakarunta sun kashe mayakan Boko Haram 134 a farmakin da ta kai musu a arewa maso gabashin kasar.
A wani sako da ta wallafa a shafinta na Twitter, rundunar ta kara da cewa ta kama manyan masu bai wa kungiyar Boko Haram bayanai 16.
Ta ce mayakan na Boko Haram sun taru ne a wani wuri da bisa kuskure suka yi tsammani tudun-mun-tsira ne inda dakarun sojin sama suka yi musu ruwan wuta kuma suka yi musu ta'adi mai yawa.
"A daya daa cikin wadannan hare-hare na atilari da aka kaddamar tsakanin raar 1 zuwa 2 ga watan Mayu, dakarun KANTANA JIMLAN, sun lalata motocin da ake haba bindigogi 7 na Boko Haram sannan suka kashe mayakan Boko Haram 78, a cewar rundunar.
Ta kara da cewa dakarunta sun kashe karin 'yan Boko Haram 56 a yankin Damboa.
"Kamar yadda bayanan sirrinmu suka nuna, kadan ne daga cikin 'yan ta'addar suka tsere daga wurin da raunuka, kuma da wahala su rayu. A wani labari mai kama da wannan, 16 daga cikin masu bai wa Boko Haram bayanai sun fada tarkon dakarunmu ciki mako biyu da suka wuce," a cewar sanarwar.