Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

'Za mu dauki ma'aikata 1,000 a kowacce karamar hukumar Najeriya'

Wannan shafi yana kawo muku bayanai kai tsaye dangane da annobar korona da ke ci gaba da yi wa duniya fyadar 'ya'yan kadanya.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Buhari Muhammad Fagge, Awwal Ahmad Janyau and Umar Mikail

  1. An kori masu sharar a filin jirgin sama na Kenya an barsu kara zube

    Wani bidiyon masu shara a filin jirgin sama na Kenya da ake zargin an kore su daga aiki ranar Talata ya janyo cece-kuce a intanet.

    Ma'aikatan sun ce sun je aiki a ranar da daddare a filin jirgi na Jomo Kenyatta da ke Nairobi babban birnin kasar, amma sa'o'i hudu bayan nan an umarce su da su ba da katin shaidarsu na tsaro kafin a koresu daga cikin ginin filin jirgin.

    Babu wani karin bayani da aka yi musu game da korar ta su, an umarce su ne kawai da su tafi gida.

    Yayin da ake fama da dokar hana fita, wadda aka sanya domin yaki da cutar korona a kasar, sun zauna tsahon dare cikin sanyi a wajen.

    Masu sharar wadanda suka ce kamfanin share-share na Colnet ne ya dauke su aiki, sun nemi gwamnati ta shiga wannan batu.

    BBC ta nemi jin ta bakin kamfanin na Colnet sai dai ya ce zai fitar da sanarwa kan batun anjima a yau.

    A cikin bidiyon da aka sa a Tiwita daya daga cikin masu sharar na bayanin yadda ba ta iya samun kula da yaranta.

  2. Coronavirus: Ghana za ta bude filayen jirgin sama

    Ministan sufurin jiragen sama na kasar Ghana, ya ce a karshen mako ne ake sa ran komawa zirga-zirgar jiragen a cikin gida.

    Joseph Kofi Adda ya ce filayen jiragen sama na Kotoka da ke birnin Accra da na Kumasi duk an yi musu feshin gusar da datti.

    To sai dai ministan ya ce dole a samu tazara tsakanin fasinjoji da sa takunkumi da kuma tabbatar da amfani da man goge datti.

    A ranar 30 ga watan Maris ne dai aka fara rufe kasar.

  3. Daruruwan fursunoni sun kamu da cutar korona a Morocco

    An samu karin masu dauke da cutar korona 313 a gidajen yarin Morocco bayan da aka yi gwaji.

    Hukumomi sun ce gidan yari na Quarzazate d ake tsakiyar kasar ya samu masu 303 cutar ta korona, inda fursuna 10 suka kamu da cutar a gidan yarin Oudaya da ke Marrakesh da kuma gidan yarin Ksar Kebir da ke gabashin kasar.

    Mafi yawancin mutanen da cutar ta kama fursunoni ne duk da cewa cutar ta shafi wasu ma'aikatan gidan yarin.

    Morocco dai na da mutum 80,000 a gidajen yari. A farkon watan Afrilu ne dai gwamnatin kasar ta yi wa fursunoni 5,654 afuwa da manufar hana bazuwar cutar korona.

    Kasar Morocco na da mutum 4,252 masu dauke da cutar, inda mutum 165 suka mutu.

  4. Budurwar Boris Johnson ta haihu

    Firai Ministan Burtaniya, Boris Johnson da budurwarsa, Carrie Symonds sun sanar da samun haihuwar da namiji.

    Mai magana da yawun Firai Ministan da abokiyar zamansa, ta ce uwar da danta duk suna cikin koshin lafiya.

    Mista Johnson mai shekara 55 da Symonds mai shekara 32 sun sanar tun a watan Maris cewa suna sa ran samun da a farkon bazara, inda kuma aka yi musu baiko a karshen shekar

    Mista Jonson dai ya yi fama da cutar korona inda ya killace kansa na wasu 'yan makonni kafin daga bisani a kai shi bangaren kulawar gaggawa a asibit lokacin da jikin nasa ya tsananta.

    Daga karshe Boris Johnson ya warke daga cutar.

  5. Coronavirus: Mutum uku sun mutu a Sokoto

    Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya sanar da mutuwar mutum uku sakamakon cutar korona.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Muhammad Bello ya fitar, Gwamna Tambuwal ya ce dukkanin mutum ukun da suka mutu na da wasu cutuka da ke damun su kamar cutar Suga da Asma da hawan jini.

    Rahotanni dai na cewa cikin wadanda suka mutu har da mataimakin shugaban jami'ar Usman Danfodio da ke Sokoto, Farfesa Lawali Abubakar Kwatarkwashi.

    Farfesa Kwatarkwashi wanda malami ne a tsangayar koyar da aikin noma na jami'ar ya rasu ne a daren jiya Talata

  6. Coronavirus: Za a rinka bai wa 'yan Malawi kudin wata a lokacin kulle

    Shugaban Malawi, Peter Mutharika ya sanar da shirin gaggawa na tallafa wa mutanen da ke fama da cutar korona a kasar.

    Magidanta za su rinka karba kwacha dubu 35 a kowane wata kwatankwacin $47 ta hanyar wayar hannu. Za a dai a fara wannan shiri ne a watan Mayu mai kamawa.

    Wannan sanarwa dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da wata babbar kotu a kasar ta yanke hukuncin hana gwamnati kara tsawaita dokar kulle ta mako uku

    Masu rajin kare hakkin dan adam dai sun sha kokawa cewa kasar ba ta ware wani shiri na tallafa wa talakawan da dokar kullen ta fi shafa ba.

  7. IMF zai bai wa Najeriya tallafin dala bilyan 3.4 domin yaki da korona

    Asusun Lamuni na Duniya, IMF ya amince da bai wa Najeriya wani tallafin gaggawa domin taimakon kasar wajen yaki da cutar korona da kuma tayar da komadar tattalin arzikinta da ya ke yin kasa sakamakon faduwar farashin mai a kasuwar duniya.

    Kudin da suka kai dala bilyan 3.4 su ne mafi girma da Asusun ya bai wa wata kasa da annobar korona ta dabaibaye.

    Asusun ya sanar da tallafin kudin ne a ranar Talata jim kadan bayan da majalisar dokokin Najeriyar ta amince wa Shugaba Buhari cin bashin dala bilyan 2.3 a cikin gida domin cike gibin kasafin kudin kasar da ya samu tawaya saboda faduwar farashin mai.

  8. Coronavirus: Magajin Garin New York ya soki jana'izar da Yahudawa suka yi

    Magajin Birnin New York, Bill de Blasio ya soki yadda wasu Yahudawa suka gudanar da taron binne wani fitaccen malamin addinin Yahudu da ya mutu sakamakon cutar korona.

    Mista De Blasio ya je makabartar domin tarwatsa mutanen.

    Ya rubuta a shafinsa na Twitter cewa irin "irin wannan taron jama'a bai halasta a wannan yanayi", inda ya kuma yi gargadin cewa hakan ka iya mayar da hannu agogo baya dangane da alkaluma masu cutar korona.

    Birnin dai na da mutum 17,000 da suka mutu sakamakon cutar ta korona.

  9. Coronavirus: Ana ci gaba da zanga-zanga a Lebanon

    An ci gaba da arangama cikin dare na biyu tsakanin jami'an tsaro da masu zanga-zanga a Tripoli, birni na biyu mafi girma a Lebanon.

    Masu zanga-zanga sun cinna wuta kan bankuna bayan jana'izar wani takwaransu dan shekara 26, da ya mutu sakamakon harbin bindiga.

    'Yan sanda sun yi amfani da barkonon tsohuwa don tarwatsa masu zanga-zangar da ke jifa da duwatsu.

    Matakan kulle saboda annobar korona sun kara ta'azzara matsalolin tattalin arziki a Lebanon, inda farashi ke hauhuwa kuma darajar kudin kasar ke ci gaba da faduwa kasa warwas.

  10. Sabon salon dakile cutar korona a Uganda

    Shugaba Yoweri Museveni na Uganda ya bullo da sabbin matakan dakile yada cutar korona ta hanyar direbobin motocin daukar kaya bayan gwaji ya nuna cewa wasu fiye da 20 da suka shiga kasar daga Kenya na dauke da cutar.

    Ba za a bar direbobi su rika daukar fasinjoji ba ko su kwana a otel ko gidajen wasu mutane.

    Gwajin cutar ta korona ala tilas tuni ya haddasa cunkoson dumbin ababen hawa a kan iyaka tsakanin Kenya da Uganda.

    An dai ce direbobin motocin daukar kaya da yaransu a Kenya kan sha zaman jiran dogon layi tsawon kwanaki don yi musu gwajin korona kafin a bari su tsallaka zuwa Uganda.

    Hanyar Mombasa mai tashar jirgin ruwa a Kenya, muhimmiya ce ga sufurin abinci, magunguna da sauran kayan tilashin rayuwa zuwa Uganda da Rwanda da Sudan ta Kudu da Jamhuriyar Dimokradiyyar Kongo.

  11. Mutum milyan daya sun kamu da cutar korona a Amurka

    Sabbin alkaluma sun nuna cewa annobar korona ta kashe Amurkawa fiye da yakin Biyatnam. Alkaluman dai sun nuna cutar ta kashe Amurkawa sama da dubu 58, kuma ta harbi fiye da mutum miliyan daya a kasar, kusan kashi daya cikin uku na daukacin adadin mutanen da suka kamu da cutar a fadin duniya.

    Bayanan sun zo ne daga Jami'ar Johns Hopkins, amma ana jin cewa lissafin ya gaza ainihin yadda lamarin yake.

    Da aka tambaye shi kan miliyan daya na yawan masu cutar da Amurka ta cimma, Shugaba Trump ya ce hakan ta faru ne saboda Amurka ta gudanar da gwaji mai yawan gaske.

  12. Budewa

    Masu bibiyarmu barka da warhaka. Ya ya mu ka ji da alhinin wannan annoba ta korona? Allah ya kare mu baki daya wadanda kuma suka mutu Allah ya jikan su. Da fatan yau ma kamar kullum za ku kasance da shafin bbchausa.com domin samun bayanai kai tsaye kan wannan annoba a sassan duniya. Mun gode.