Buhari ya ce za a yi binciken mace-macen Kano
Shugaban Najeriya ya bayyana damuwa kan mace-macen da aka samu a jihar Kano da ke arewacin kasar.
Shugaban ya ce ya aika da tawaga domin gudanar da bincike tare da kulle jihar na tsawon mako biyu.
Kalaman shugaban na zuwa bayan yawan mace-macen da ake samu a kano fiye da kowane lokaci a baya.
Al’ummar jihar na cikin hali na rashin tabbas kan abin da ya haifar da mace-macen yayin da ake cikin wannan yanayi na annobar korona.
Wasu na tunanin cutar korona ce ta shiga al’umma kuma ta ke yi wa jihar illa.
A cikin mako guda fitattun mutane da masu shekaru sun kwanta dama a kusan dukkanin unguwannin jihar.
Amma hukumomi a jihar sun ce mace-macen da aka samu bay a da alaka da cutar korona. Sun ce cutuka kamar hawan jini da ciwon suga da sankarau da zazzabin maleriya na iya haifar mace-macen.
Kano ita ce ta uku cikin jerin jihohin Najeriya da ke fama da cutar korona.