Covid-19: 'Jami'an tsaron Rwanda suna yi wa mutane fyade'
- Marubuci, Mary Harper
- Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Edita a Afrika, BBC World Service
Kungiyar kare hakkin dan adam ta zargi jami'an tsaron Rwanda da laifin kisa, da fyade da kuma kama mutane tun lokacin da aka kakaba dokar hana fita.
Kungiyar Human Rights Watch ta ce an harbe akalla mutum biyu a kudancin lardin Nyanza.
Ta kara da cewa an kulle mutanen da ake zargi da karyar dokar hana fitan a filayen wasa, sannan wasu mutane sanye da kakin soji sun yi wa mata fyade.
Kazalika an kulle 'yan jaridar da suka bayar da labaran zargin yi wa matan fyade.
Rundunar sojin Rwanda ta ce ta soma bincike kan zarge-zargen, kuma ta kulle mutum biyar da ake zargi da hannu a zarge-zargen.