Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Burtaniya za ta fara gwajin riga-kafin cutar korona

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a duniya baki daya dangane da annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir and Awwal Ahmad Janyau

  1. Coronavirus: Gidajen jaridu a Najeriya na neman 'durkushewa'

    A Najeriya yayin da ake cikin mako na uku bayan da gwamnatin kasar ta sanya dokar hana zirga-zirga sanadin cutar korona, gidajen rediyo masu zaman kansu a arewacin kasar na fuskantar barazanar durkushewa.

    Yanzu haka dai kungiyar masu gidajen rediyon a kasar ta fara neman agaji don kauce wa matsalolin da ka iya jefa 'ya'yanta cikin halin ha'ula'i.

    Shugaban kungiyar, kuma mamallakin Liberty da ke Abuja, Tijjani Ramalan ya shaida wa BBC cewa "mu a nan Najeriya babbar hanyar samun kudin shigarmu ita ce samun tallace-tallace amma kamfanonin da ke ba mu tallar sun shaida mana cewa ba za su iya ci gaba da mu'amala da mu ba saboda cutar korona."

    Ya kara da cewa "yanzu ba ma iya biyan ma'aikatanmu kuma bashi ya yi mana yawa. Muna kiran gwamnati da ta taimaka mana da rance daga asusu na musamman na tallafa wa kamfanoni irinsu domin tayar da komada."

  2. Ranar Laraba za mu kulle jihar Borno saboda bullar cutar korona

    A jihar Borno al'ummar jihar na can na shirye-shirye don tunkarar zaman gida na mako biyu kamar sauran 'yan uwansu na wasu jihohin kasar sanadin bullar cutar korona a karshen mako.

    A yammacin jiya ne dai gwamnan jihar ya sanar da aniyar gwamnatin na kakaba dokar zaman gida daga ranar Laraba.

    Mai magana da yawun gwamnan jihar, Isa Gusau, ya ce an bai wa 'yan jihar kwana biyu ne domin shiryawa tsaf kafin ranar Laraba lokacin da za a rufe jihar.

    Kafin bullar cutar a jihar dai gwamnatin jihar ta sha kokarin daukar matakan kariya ga dubban 'yan gudun hijrar da ke zaune a sansanoni daban-daban a fadin jihar.

  3. Cutar korona ta bulla jihar Sokoto a karon farko

    A karon farko cutar korona ta bulla cikin jihohin Sokoto da Gombe dukansu a arewacin Najeriya.

    Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Sokoto, jihar da cutar ta bulla a baya-bayan nan ya gabatar da jawabi a wani taron manema labarai inda ya ce za a mayar da mutumin da cutar ta shafa zuwa cibiyar kebe marasa lafiya ta Amanawa.

    Hukumar dakile cututtuka masu yaduwa a Najeriya ta ce adadin masu fama da cutar ya zuwa daren Litinin ya kai 665, bayan samun karin mutum 38 masu dauke da cutar a fadin kasar.

    Sai dai wani labari mai karfafa gwiwa shi ne mutum 18 ne rigis suka warke daga cutar a ranar Litinin din cewar alkaluman NCDC, inda yanzu haka mutum 198 daga cikin 665 suka warke.

    Wannan karo jihar Kano ce ta fi samun mutanen da cutar ta sake kamawa da 23, inda adadin masu annobar ya kai 59 a cikin kwana 10.

  4. Da dama 'yan jamhuriyar Nijer ba su yadda akwai cutar korona ba

    Da alama har yanzu mutane da dama a nahiyar Afirka ba su gamsu da kasancewar cutar korona ba duk kuwa da irin yadda cutar ke kayar da jama'a.

    A jamhuriyar Nijer ma na fama da irin wannan matsala inda da dama daga cikin 'yan kasar sun ki su amince da cewa akwai ma cutar hakan ya sa su bijire wa dokokin kariya da gwamnatin kasar ta saka.

    A jamhuriyar Nijar mutum 655 ne adadin wadanda suka harbu da cutar korona inda daga ciki 124 sun warke sannan 20 sun mutu.

    A birnin Yamai duk da rufe baki da hanci ya zamo doka da hukumomin birnin suka tillasta mafi yawan mazauna birnin sun yi fatali da ita.

  5. Coronavirus: Shugaba Trump zai hana 'yan cirani shiga Amurka

    Shugaba Donald Trump ya ce zai rattaba hannu kan wata dokar dakatar da baki shiga Amurka.

    Ya ce an dauki matakin ne saboda cutar korona da kuma bukatar kare ayyukan Amurkawa. Sai dai bai yi karin haske ba a sakon da ya wallafa a shafin Tiwita.

    Amurka ta bi sahun Canada da Mexico wajen tsawaita takunkumin rufe iyakoki musamman kan tafiye-tafiyen da basu zama dole ba har sai tsakiyar watan Mayu.

    A ranar Litinin ne Amurka ta yi barazanar ci gaba da korar bakin da ta gania iyakar kasar da Mexico.

  6. Farashin danyen man Amurka ya fadi warwas saboda cutar korona

    Farashin man Amurka ya yi gagarumar faduwa a karon farko a tarihi.

    Hakan na nufin dillalan man fetur sai sun biya masu saye don su raba su da shi saboda ba su da wajen adana man sannan rufe rijiyoyin man abu ne da ake ganin akwai tsada.

    BBC ta gano cewa matakin kasashe masu samar da danyen mai a kungiyar OPEC na rage yawan man da suke hakowa bai wani taka rawar gani ba na magance matsalar.

    A jawabin da Shugaba Trump ya ke yi duk rana, ya ce Amurka za ta kara miliyan 75 na gangar mai ga ma'ajiyarta ta kasa.

    Bukatar man a duniya ta ragu sosai saboda matakan kulle sun sa mutane na zaman gida

  7. Coronavirus na barazana ga 'yancin 'yan jarida a duniya

    Kungiyar 'yan jarida ta Reporters without Borders ta yi gargadin cewa annobar coronavirus na kara barazana ga 'yancin kafafen watsa labarai a fadin duniya.

    A rahoton shekara-shekara kan 'yancin 'yan jarida a duniya, kungiyar ta ce akwai dangantaka tsakanin matsayin kasa a jadawalin da kuma yadda take yaki da annobar.

    Kungiyar ta ce a China da aka bayyana a matsayin kasar da ta fi cin zarafin 'yan jarida, gwamnati ta na tace rahotannin da ake ba da wa kan annobar korona.

    Rahoton ya kuma bayyana wasu tsauraran matakan hana zirga-zirga a Iran da Iraki da kuma Hungary da aka tanadarwa masu yada labaran karya kan annobar hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekara biyar.

  8. An kafa gwamnatin gambiza a Israila don yaki da cutar korona

    An kafa gwamnatin gambiza a Isra'ila domin yaki da annobar coronavirus.

    A shekara uku da rabin farko na yarjejeniyar, Benyamin Netanyahu zai ci gaba da zama Firai Minista duk da zarge-zargen cin hanci da ake masa.

    Daga bisani kuma zai mika mulki ga abokin hamayyarsa Benny Gantz.

    Yarjejeniyar dai ana ganin za ta kawo karshen wani lokaci na rashin tabbas a tarihin rikicin siyasar Isra'ila wanda nasara ce ga Mista Netanyahu wanda zai ci gaba da zama kan kujerar mulki duk da zargin aikata laifin rashawa da cin hanci.

    A baya dai an gudanar da zabuka har sau uku ba tare da samun ci gaba ba.

  9. Ana samun raguwar masu cutar korona a Italiya

    A karon farko, an samu raguwar mutanen da aka tabbatar sun kamu da cuar korona a Italiya.

    Hukumomi sun sanar da hakan bayan da aka samu mutane kalilan da ke kwance a dakin ba da kulawa ta musamman.

    Sun ce lamarin wani ci gaba ne musamman a kasar da cutar ta fi yin kamari a Turai duk da samun karuwar mutanen da suka mutu zuwa sama da mutum dubu 24.

    Faransa ta zama kasa ta hudu da ta samu yawan mutanen da suka mutu da suka wuce dubu ashirin - ta bi sahun Italiya da Spaniya da kuma Amurka.

  10. 'Yadda muke samun karuwar mamata a Kano'

    Daya daga cikin masu kula da makabartar da ya nemi a boye sunansa ya ce tun daga ranar Juma'ar da ta gabata zuwan safiyar Litinin an binne kusan mutane 50 a makabartar Dan Dolo, wanda rabon su da su sami irin hakan tun lokacin da Boko Haram ta kai hari babban Masallacin Juma'a da ke Kano a shekarar 2011.

    A makabartar Gidan Gona da aka fi sani da Makabartar Tarauni, wasu daga cikin masu kula da makabartar ya shaida wa BBC cewa tun kwanaki biyar da suka gabata yawan wadanda ake binnewa a makabartar ya karu.

    Ya kara da cewa a safiyar Litinin kadai iya mutum hudu ne aka binne a makabarta, amma jumulla adadin wadan da aka kai makabartar sun kai kusan 55 sannan kusan mafi yawancin lokutan zafi da farkon kowane azumi sukan sami yawan gawarwakin da akan binne amma basu kai na wannan shekarar ba.

    Wakilin BBC da ya ziyarci Makabartar Dandolo da safiyar ranar Litinin ya ce ya hangi rukunin mutum uku da suka je makabartar daga unguwanni daban-daban domin kai gawarwaki don binnewa.

    Farfesa Isa Sadik Abubakar, shugaban sashin cututtuka masu yaduwa na jami'ar Bayero da asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano ya ce a fahimtarsu watakila yawan mace-macen ba ya fi na da bane.

    Saboda "idan asibiti ba ya hayyacinsa ba ya bayar da taimako yadda aka saba, babu mamaki irin wadannan mutanen su shiga wani hali na shan wuya watakila ma a samu wasu daga cikinsu su rasu," in ji Farfesan.

    Ita ma gwamnatin jihar ta musanta cewa ana samun karuwar mace-mace.