Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da suka faru a Najeriya da sassan duniya ranar 16/04/2020

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a duniya baki daya dangane da annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya and Umar Mikail

  1. Covid-19: Mutum 83 sun warke a Ghana

    Hukumomi a Ghana sun ce mutum 83 sun warke daga cutar korona.

    A cewar hukumar lafiyar kasar, utum 17 na jiran sakamakon gwajin da aka yi musu wanda ake sa ran zai tabbatar su ma sun warke daga cutar.

    Ana yin gwaji sau biyu zuwa uku kan mutanen da ke fama da cutar kafin a tabbatar sun warke.

    Ya zuwa ranar Alhamis, an tabbatar mutum 642 suna dauke da cutar inda ta yi ajalin mutum takwas.

  2. Wasu mutum hudu sun mutu a Saudiyya

    Karin mutum hudu sun mutu a Saudiyya sakamakon cutar korona a cikin awa 24 da suka gabata, abin da ya kai jumullar adadin zuwa 84, a cewar ma'aikatar lafiyar kasar.

    Jaridar Saudi Gazette ta ruwaito mai magana da yawun ma'aikatar yana cewa mutum hudun da suka mutu ba 'yan Saudiyya ba ne kuma suna fama da wasu cutukan na daban.

    Kazalika shekarunsu ya kama daga 35 zuwa 89.

    Kakakin ma'aikatar ya ce an samu sabbin mutum 518 da aka tabbatar sun kamu da cutar a Saudiyya, wanda jumullar adadinsu ya kai 6,380.

    Daga cikinsu, 990 sun warke bayan samun rahoton 59 da suka warke a cikin sa'a 24 da suka wuce, a cewar ma'aikatar lafiyar.

    Ministan Lafiya Dr Tawfiq Al-Rabiah ya ce bisa binciken da kwararru suka gudanar, mutum 200,000 ka iya harbuwa da cutar a cikin 'yan makonni masu zuwa a kasar.

  3. Dokar hana fita: Kanawa sun yi wa kasuwanni tsinke

    Yayin da 'yan sa'o'i suka rage dokar hana fita ta fara aiki a fadin Jihar Kano da ke arewacin Najeriya, mazauna jihar sun yi wa kasuwanni tsinke domin tattala abubuwan amfani saboda kada a rufe da su.

    Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya ce dokar ta mako daya ce domin kare yaduwar cutar.

    Mutum 21 ne suka kamu da cutar zuwa yanzu a Kano, a cewar ma'aikatar lafiyar jihar, kuma daya daga ciki ya mutu.

  4. Za a ci gaba da koyar da 'yan sakandare ta Whatsapp a Nijar

    Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta bayyana cewa za'a ci gaba da koyar da darusa a matakin sakandare ta dandalin Whatsapp domin kada a yi asarar zangon karatu na bana.

    Shugaban hukumar daraktocin illimin sakandare ne ya umarci daraktocin jihohi da su kirkiri zauruka a Whatsapp wato groups a mataki hudu - daya a mataki na kasa, biyu a matakin jihohi, daya a matakin kowacce makaranta.

    An dauki wannan mataki ne sakamakon rufe makarantun da aka yi a kokarin da kasar keyi na hana yaduwar cutar korona da ke ci gaba da bazuwa a kasar.

    Mutum 584 ne suka kamu da korona a Nijar sannan 97 suka warke, yayin da 14 kuma suka rasa rayukansu.

    Sai dai wakiliyar BBC a birnin na Yamai, Tchima Illa Issoufou ta ce jama'a a birnin Yamai ciki har da daliban da iyayensu sun bayyana mata cewa abin da kamar wuya a kasar.

  5. Malamai sun amince da dakatar da sallar Juma'a a Kano

    Malamai a jihar Kano da ke arewacin Najeriya sun amince da dakatar da sallar juma’a a daukacin masallatan jihar, a yayin da dokar hana fita da gwamnati ta saka ke fara aiki a yau Alhamis.

    Malaman dai sun gudanar da taron nasu ne a Africa House da ke fadar gwamnatin Kano ranar Alhamis, karkashin kwamitin kar ta kwana na cutar korona da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya kafa.

    Idan an jima ne dokar hana fita da gwamnatin jihar ta kafa za ta fara aiki, wadda za a shafe tsawon mako guda.

    Shawararin malaman dai na zuwa ne bayan da hukumomi a jihar Kano suka sanar da mutuwar wani mutum mai dauke da cutar korona a jihar, yayin da adadin wadanda suka kamu da cutar ya kai mutum 21.

    Wakilinmu na Kano Khalifa Shehu Dokaji ya ce Malaman sun yi nazarin harkokin rayuwar al'umma ne wadanda ke da nasaba da taron jama'a da nufin bayar da fatawa, inda suka amince da dakatar da Sallar Juma'a a masallatan jihar da kuma tarukan da ake yi da suka shafi karatu a lokacin watan Ramadan, don hana yaduwar cutar korona a tsakanin al'umma.

    Dr. Ibrahim Mu’azzam mai Bushira shi ne sakataren karamin kwamitin malamai da kwamitin kar ta kwana na coronavirus ya kafa, wanda ya ce malaman sun amince da a dakatar da gabatar da Sallar Juma’a don gudun kada wani da yake dauke da cutar ya yada ta a tsakanin al’umma.

  6. NCDC na horar da ma'aikatan lafiya kan korona a Najeriya

    A ci gaba da kokarinta na habaka hanyoyin yaki annobar koirona a nNajeriya, hukumar NCDC mai yaki da cutuka masu yaduwa ta horar da ma'aikatan lafiya a Jihar Anambra a wanna mako.

    An yi aikin horarwar ne a asibitin koyarwa na Chukwuemeka Odumegwu da ke jihar.

    Zuwa yanzu, Najeriya na da wadanda suka harbu da cuytar ta korna guda 407, mutum 128 sun warke sai kuma 12 da suika rasu.

  7. An samu karin masu dauke da cutar korona a Tanzania

    Ma'aikatar lafiyar Tanzania ta bayar da sanarwar samun adadi mafi yawa na mutanen da suka kamu da cutar korona a kasar, inda ta tabbatar da mutum 29 na dauke da cutar.

    A cikinsu, an gano mutum 26 suna birnin kasuwancin kasar, Dar es Salaam, biyu kuma a garin Mwanza da ke arewa maso kudancin kasar sannan mutum daya a Kilimanjaro.

    Ranar Laraba, ma'aikatar lafiya ta yankin Zanzibar ta sanar da karin mutum shida da suka harbu da cutar - adadi mafi girma da aka samu tun da cutar ta bulla a yankin.

    Yanzu masu dauke da cutar korona a Tanzania sun kai 88.

    Ba kamar sauran kasashen Gabashin Afirka ba, Tanzania ba ta takaita zirga-zirgar jama'a ba kodayake ta dauki matakan hana taruwar jama'a.

    Kakakin Majalisar Dokokin kasar Job Ndugai ya ce daukar matakai irin na Turai wajen yaki da cutar korona - kamar hana mutane fita daga gida - suna iya jefa 'yan kasar Tanzania cikin hatsari.

  8. Abubuwan da suka faru game da cutar korona zuwa yanzu

    • Bayanai na baya bayan nan daga Jami'ar Johns Hopkins ta Amurka da ke bibiyar yaduwar cutar korona ta wallafa sun nuna cewa mutum 2,065,906 sun kamu da cutar a duniya. Mutum 137,124 sun mutu sakamakon cutar, sai kuma 517,444 da suka warke.
    • Tawagar likitocin China ta tafi kasashen Habasha da Burkina Faso domin bayar da tallafi a kokarin yaki da cutar korona, a cewar gidan talbijin din kasar na CGTN.
    • Ministar Kudin Najeriya Zainab Shamsuna Ahmed ta ce da ma asusun ba da lamuni na duniya IMF ba ya bin Najeriya bashi kuma dalilin da ya sa bai saka ta cikin kasashen da za su ci gajiyar tallafin korona ba Kenan. Sai dai ministar ta ce IMF na duba wata bukatar ta daban da Najeriya ta nema.
    • Ma’aikatar lafiyar kasar Iran ta ce mutum 1,606 ne suka kamu da cutar korona a cikin sa’a 24 da suka gabata sannan 92 da suika mutu.Jumullar wadanda suka kamu sun kai 77,995 sannan wadanda suka rasun sun kai 4,869.
    • Shugaban Kungiyar Tarayyar Turai Ursula von der Leyen ya nemi afuwar kasar Italiya a madadin kungiyar bisa yadda suka gaza tallafa wa kasar a lokacin da annobar korona ta fantsama a kasar.
  9. COVID-19: An kama ministan da ya sayi giya lokacin zaman gida

    'Yan sanda a Lesotho sun ce za su tuhumi wani minista da aka gani a kyamarar tsaro yana sayen barasa lokacin da aka tilasta wa mutane zaman gida don hana yaduwar cutar korona.

    Lesotho - kamar Afirka ta Kudu - ta haramta sayar da barasa lokacin tabbatar da dokar hana zirga-zirga.

    Bidiyon da ya nuna Lehlohonolo Moramotse, ministan 'yan sanda da tsaron jama'a, yana karbar katon-katon na giya a wani kantin sayar da barasa ya watsu tamkar wutar daji a shafukan zumuntar kasar makon jiya.

  10. A ina aka fi samun masu dauke da coronavirus?

    Ku kalli wannan hoton domin ganin kasashen da cutar korona ta fi mamaya a duniya.

  11. COVID-19: Likitocin China sun tafi Afirka don bayar da agaji

    Tawagar likitocin China ta tafi kasashen Habasha da Burkina Faso domin bayar da tallafi a kokarin yaki da cutar korona, a cewar gidan talbijin na China Global Television Network.

    Ba a bayyana adadinsu ba, amma sun fito ne daga lardunan Sichuan da Tianjin Municipality.

    Ma'aikatar harkokin wajen China ta ce sun bar kasar zuwa Afirka ne ranar Alhamis.

    An ambato kakakin ma'aikatar wajen China Zhao Lijian yana cewa likitocin za su yi bayani kan yadda suka dakile cutar a kasarsu, sannan su bayar da koyar kan yadda kasashen biyu za su kawar da cutar korona.

    Najeriya ma ta shigo da likitocin kasar China 18 domin su taimaka mata wajen yaki da cutar, ko da yake likitocin kasar sun bayyana rashin jin dadinsu.

    Kungiyar likitoci ta kasar ta ce zai fi kyau a yi amfani da likitocin da ba su da ayyuka ko kuma wadanda aikin bai ishe su ba, domin yaki da cutar korona.

    Rahotanni sun ce an kori daruruwan 'yan Afirka daga otal-otal dinsu a birnin Guangzhou domin gudun kada su yada wa mutane cutar korona.

    Ministan harkokin wajen Najeriya ya bayyana rashin jin dadinsa kan matakin, inda ya ce a shirye kasarsa take ta kwashe 'ya'yanta daga China.

  12. Coronavirus: Tattaunawa da Kwamishinan Lafiya na jihar Bauchi

    Tattaunawa da Kwamishinan Lafiya na jihar Bauchi Dr Aliyu Mohammed Maigoro kan cutar korona tare da Fauziyya Kabir Tukur a shafinmu na Fabook.

  13. Me ya sa Najeriya ba ta cikin kasashen da IMF ta yi wa sassauci?

    A makon nan ne Asusun Lamuni na Duniya ya ce zai jinkirta wa matalautan kasashe 19 a Afirka biyan bashin da yake bin su zuwa wata shida domin su yi amfani da kudin wajen yaki da cutar korona.

    Kasashen sun hada da Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Dimkradiyyar Congo.

    Amma Najeriya ba ta ciki, lamarin da ya sa wasu suke tambayar dalilin da ya sa hakan.

    Sai dai ministar kudin kasar, Zainab Shamsuna Ahmed, ta ce Najeriya bata samu sassaucin bashi daga Asusun Lamuni na Duniya, IMF, ba saboda Asusun ba ya bin ta bashi.

    A sakon da ta wallafa a Twitter ranar Alhamis, ta ce "tun da IMF ba ta bin Najeriya bashi, babu bukatar a yafe mata shi".

  14. Dakunan ajiyar gawarwaki sun cika makil a Ghana saboda coronavirus

    Dakunan ajiyar gawarwaki sun cika makil a Ghana yayin da iyalai suka daina binne gawarwakin 'yan uwansu da kansu saboda dokar nesa-nesa da juna da kuma haramta yin tarukan jama'a domin dakile cutar korona.

    Iyalai da 'yan uwan mamata sun ce gara su jira har lokacin da za a janye dokar hana fita sannan su gudanar da bukukuwan binne 'yan uwan nasu, a cewar kafofin watsa labarai na kasar.

    Masu aiki a dakunan ajiyar gawarwarki sun ce dakunan basu taba cika kamar wannan lokaic ba.

    Lamarin ya so fin karfin wasu dakunan ajiyar gawarwarki kamar na asibitin Pantang da ke Greater Accra, inda aka ambato mahukuntansa suna cewa ba za su ci gaba da karbar gawarwaki ba.

  15. Har yanzu ban warke daga coronavirus ba - El-Rufai

    Gwamnan jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya, Nasir Ahmad El-Rufai, ya ce har yanzu bai samu sauki daga cutar korona ba.

    El-Rufai ya bayyana haka ne a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter da yammacin ranar Laraba.

    "Har yanzu ban warke daga cutar covid-19 ba kuma da kaina zan bayyana hakan idan na warke. Ku guji yada labaran karya ko da kuwa kuna son yi," in ji gwamnan.

    A ranar Laraba ne, gwamnatin jihar ta ce ta sallami mutum daya cikin mutane shida da suka kamu da cutar korona a jihar.

  16. Alamun Coronavirus: Abubuwan da suka kamata ku dinga yi

  17. Alkaluman baya bayan nan kan coronavirus a duniya

    Bayanai na baya bayan nan da Jami'ar Johns Hopkins ta Amurka da ke bibiyar yaduwar cutar korona ta wallafa sun nuna cewa mutum 2, 065, 906 sun kamu da cutar a duniya.

    An wallafa wadannan bayanai ne a safiyar ranar Alhamis 16 ga watan Afrilu, 2020.

    Jami’ar ta kara da cewa mutum 137, 124 sun mutu sakamakon cutar, wacce take sarkafe numfashi.

    Sai dai jami’ar ta ce mutum 517, 444 sun warke daga cutar ta korona.

    Amurka ce ta fi yawan wadanda suka kamu da cutar, inda ya zuwa safiyar Alhamis mutum 639, 664 suka kamu.

    Spaniya na biye mata da mutum 180, 659, sai kuma Italiya ta zo ta uku da mutum 165, 155, yayin da Jamus ta zo ta hudu inda cutar korona ta kama mutum 134, 753.

    A China, inda cutar korona ta samo asali, mutum 83, 402 ne suka kamu da cutar.

  18. Barkanmu da sake saduwa

      • Marubuci, Nasidi Adamu Yahya
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Hausa, Abuja

    Daga na Sashen Hausa na BBC muke yi muku barka da sake saduwa a wannan shafi. Da fatan za ku kasance tare da mu domin sanin halin da ake ake ciki dangane da cutar korona, wacce ke ci gaba da kisa a kasashen duniya.

    Baya ga batun wannan cuta, za kuma mu kawo muku sauran labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku, musamman daga kasashen Najeriya da Nijar da ma wasu sassan duniya.

    Kuna iya tafka muhawara da bayyana ra’ayoyinku a shafukanmu na sada zumunta a BBC Hausa.