Ghana ta kaddamar da wata manhajar wayoyin hannu da nufin taimaka wa hukumomi wajen gano mutanen da ake zaton sun kamu da cutar korona.
Gwamnatin kasar ta ce manhajar za ta taimaka wajen sauya salon yaki da annobar, kuma kawo yanzu an yi amfani da manhajar wajen gano kusan mutum 100 da ake ji suna da cutar.
Manhajar za ta ringa amfani da taswira ta hanyar GPS wajen bibiyar wuraren da mutum ya je, abin da zai ringa bai wa hukumomi damar gano ko mutum ya yi mu'amala da wanda aka tabbatar yana dauke da cutar.
Za kuma a yi amfani da ita wajen gano ko mutanen da aka umarta su kebe kansu suna aiki da umarnin, duk da cewa ba a san irin hukuncin da za a yi wa wadanda ba su bi umarnin ba.
Za a iya amfani da manhajar a yaruka biyar, amma da yake masu amfani da wayoyin tafi-da-gidanka na zamani basu wuce 35% ba, amfanin manhajar zai iya zama takaitacce.
Ana nuna damuwa kan batun tsaron bayanan masu amfani a manhajar, sai dai ma'aikatar sadarwa ta ce ana tabbatar da kiyaye bayanan masu amfani da manhajar.
Kawo yanzu Ghana ta yi wa mutum 37,000, sannan ta tabbatar da cewa mutum 636 sun kamu, sannan mutum takwas sun mutu.
A bangare daya kuma Asusun Lamuni na Duniya, IMF, ya tallafa wa Ghana da kusan dala biliyan daya domin taimaka mata rage dawainiyar cutar.
An sanya dokar hana fita a wasu sasssan Ghana da suka hada da babban birnin kasar Accra, sannan iyakokin kasar sun ci gaba da kasancewa a rufe.