Matasa da dama ne suka yi zanga-zanga a wajen ofishin jakadancin
Faransa da ke, Yaoundé, babban birnin Kamaru sabodakalaman "muzantawa" da shugaban
Faransa Emmanuel Macron ya yi kan Shugaba Paul Biya.
Hakan ya faru ne
bayan wani bidiyo da ya watsu a shafukan sada zumunta a karshen mako ya nuna
Shugaba Macron yana shaida wa wani mai fafutuka dan kasar a Paris cewa ya matsa
lamba kan Mr Biya domin sako shugaban ‘yan
hamayyar kasar Maurice Kamto – wanda aka sako shi daga kurkuku wata tara bayan
an kama shi a watan Oktoba na 2019.
A cikin bidiyon, an ji Shugaba Macron yana cewa “akwai hakkokin dan
adam” da ake takawa fiye da misali a kasar
Kamaru – ya yi kalaman ne kwanaki kadan bayan ‘yan bindiga sanye da kakin soji
sun kasha mutum 22 a kauyen Ngarbuh da
ke Arewa maso Yammacin kasar.
Mr Macron ya shaida
wa mai fafutukar cewa "Zan kira Shugaba Biya makon gobe kuma zan matsa
masa lamba sosai ta yadda za a kawo karshen wadannan matsaloli." .
Sai dai kalaman basu
yi wa gwamnatin Kamaru dadi ba.
Wani mai zanga-zanga ya ce "Muna
kaunar shugabanmu. Mutum ne mai son zaman lafiya."
Babu wani darasi da
Faransa za ta koya wa Kamaru kuma dole Macron ya nemi afuwa saboda cin mutuncin
da ya yi cewa shugabanmu dan barandarsa ne," a cewar wani mai zanga-zangar.
Wani kuma ya rike kwalin da aka rubuta cewa ya kamata Macron ya
rika girmama dattawa, yana mai cewa Kamaru kasa ce mai cin gashin kanta.
Mai fafutukar, Yvone Mumah Biya, ya ce gwamnatin Kamaru ce ta
daukki nauyin masu zanga-zangar.