Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Zaben Bayelsa bai inganta ba – CDD

CDD ta ce mummunan tashin hankali da aka tsara kuma aka tayar da gangan a rumfunan zabe da dama, sun hana mutane fitowa domin kada kuri'a domin tsira da rayukansu.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Haruna Kakangi

  1. Ana sayen kuri'u a Lokoja

    Wakilin BBC a Lokoja babban birnin jihar Kogi Ibrahim Isa, ya ce ana zargin jam'iyyu da sayen kuri'u.

    Ana zargin cewa jam'iyyar APC mai mulki na sayen kuri'un a kan Naira 5,000, yayin da ake zargin PDP da sayen kuri'un a kan Naira 1,000.

    Ibrahim Isa ya ce ya shaida yadda ake sayen kuri'un a wasu mazabu da ya ziyarta.

  2. APC za ta saci akwati - Musa Wada

    Dan takarar jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Kogi Musa Wada ya yi zargin cewa jam'iyyar dake hamayya da shi na mazabarsa ya kulla makarkashiyar kai hari tare da sace akwatin zabe.

    Ya fadi haka ne jim kadan bayan ya kada kuri'arsa a mazabar Ayingba da ke karamar hukumar Dekina.

  3. An saci akwati a mazabata - Dino Melaye

    Sanata Dino Melaye ya yi zargin cewa wasu 'yan daba sun saci akwati a mazabarsa jim kadan bayan ya fice daga rumfar zabe.

    Dino ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa wani ne wani matashi ne ya jagoranci matasan, inda suka rika harbi kan mai uwa da wabi.

    "Jim kadan bayan na fita daga rumfar zabe wasu tsageru suka shiga karkashin jagorancin Sunday Faleke suka rika harbin kan mai uwa da wabi sannan suka tsere da akwatin zabe."

  4. Musa Wada ya kada kuri'arsa

    Dan takarar jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Kogi Musa Wada ya kada kuri'asa.

  5. Natasha ta kada kuri'a

    'Yar takarar jam'iyyar SDP kuma mace tilo da take takarar gwamna a jihar Kogi Natasha Akpoti ta kada kiuri'arta sa'o'i kadan bayan ta ce ta kasa fitowa daga gida domin kada kuri'a saboda fargabar tashin hankali.

  6. An kai wa wakilan jam'iyya hari a mazabar Obeiba a Kogi

    Wakiliyar BBC Dooshima Abu ta ruwaito cewa wasu mutane sanye da kakin sojoji sun shiga mazabar Obeiba Ward One, karamar hukumar Okehi, inda suka fatattaki wasu daga cikin wakilan jam'iyyu.

    Wasu daga cikin wakilan jam'iyyun suna dauke da raunuka a jikinsu kuma daya daga cikinsu ya shaida mata cewa wani wakilin jamiyya ne ya yi yunkurin yin amfani da wani katin zabe shi kuma ya nuna tirjiya, sai suka rufe shi da duka har sai da ya suma.

  7. Natasha Akpoti ta kasa fitowa kada kuri'a, Yadda zabe ke gudana a Kogi da Bayelsa

    Rahotanni na cewa 'yar takarar gwamnan Kogi a jam'iyyar SDP Natasha Akpoti ta kasa fitowa daga gidanta domin kada tata kuri'ar saboda tsoron tashin hankali a mazabarta mai suna Obeiba.

    Da ma dai tun kafin yau Natasha ta sha zargin cewa APC na son ganin bayanta, inda ta yi zargin cewa matasan jamiyyar sun hana ta shiga wurin taron yarjejeniyar zaman lafiya tare da ji mata rauni a ranar Talata.

    Sai dai jam'iyyar APC a jihar ta sha musanta wannan zargi.

  8. Ana tafka ta'asa a rumfar zabe a jihar Kogi

    Wani mai sanye da katin wakilcin jam'iyyar APC kenan yake nuna wa masu zabe jam'iyyar da za su zaba a rumfar zabe tare da karbar kuri'un nasu, inda yake linkewa tare da sakawa a cikin akwatin zaben.

    Wannan abu ya faru ne a garin Okene.

  9. Dino Melaye a mazabarsa

    Sanata Dino Melaye a mazabarsa yayin da yake shirin kada kuri'a.

    Dino Melaye dai ba kuri'ar zaben gwamna kadai zai kada ba, shi ma dan takara ne a zaben kujerar sanata mai wakiltar Kogi ta Yamma, inda yake shiga takarar a karo na biyu bayan kotun sauraron kararrakin zabe ta soke wanda aka bayyana shi a matsayin wanda ya lashe a watan Fabarairu.

  10. An fara kada kuri'a a Bayelsa, Yadda zabe ke gudana a Kogi da Bayelsa

    Su ma masu kada kuri'a a jihar Bayelsa sun fara jefa nasu kuri'un a akwati mai lamba 5 ta mazabar Ward 8 da ke karamar hukumar Imiringi Ogbia.

  11. Ba a bar mata a baya ba, Yadda zabe ke gudana a Kogi da Bayelsa

    An samu fitowar Iyaye mata da yawa domin kada kuri'arsu a garin Okene na jihar Kogi.

  12. Yadda zabe ke gudana a Kogi da Bayelsa

    INEC ta bayyana wasu hanyoyi da masu zabe za su iya gano ru,mfar zaben da ya kamata su jefa kuri'a a jihohin Bayelsa da Kogi.

    Ga lambobin da za a kira nan:

    0700 2255 4632 09050858629 08180958715

    Akwai kumna sakon email da za a iya turawa - a duba hootn da ke kasa.

  13. Yadda zabe ke gudana a Kogi da Bayelsa

    A jihar Bayelsa kuwa, INEC ta ce akwai mutum 923,182 da suke da rajistar zabe a kananan hukumomi takwas da kuma wuraren yin rajistar guda 105, sai kuma rumfar zabe guda 1804.

    Jam'iyya 46 ne za su fafata a zaben, inda 43 na 'yan takarar maza ne yayin da mata uku ne kacal.

    Hukumar ta ce kashi 93% na masu rajistar ne suka karbi katin zabensu na dindindin.

    Zuwa yanzu dai ana ci gaba da rarraba kayayyakin zabe ne.

  14. Yadda zabe ke gudana a Kogi da Bayelsa

    A jihar Kogi 'yan takara 23 ne ke kokawar lashe kujerar gwamnan jihar kuma za a yi zaben ne a rumfunan zabe sama da 2,500, kamar yadda hukumar zabe INEC ta jihar ta bayyana.

    Masu kada kuri'a a mazabar Attah Frontage da ke garin Lokoja suna kada kuri'arsu ba tare da wani tashin hankali ba.

  15. Yadda zabe ke gudana a Kogi da Bayelsa

    Tuni aka fara jefa kuri'a a jihar Kogi kuma gwamna mai-ci dan takarar APC Yahaya Adoza Bello ya jefa tasa kuri'ar a mazabarsa.

  16. Yadda zabe ke gudana a Kogi da Bayelsa

    Jama'a barkanku da war haka, barka da safiyar ranar zaben gwamna a jihohin Kogi ta Arewa ta Tsakiyar Najeriya da kuma Bayelsa ta Kudu maso Kudancin Najeriya.

    Umar Mikail ke maku fatan an tashi lafiya.