Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

PDP ta nemi a soke zaben Osun

Labarai da sharhi game da karashen zaben gwamnan Osun inda dan takarar jam'iyyar PDP da na APC suka kara.

Rahoto kai-tsaye

Abdulwasiu Hassan

  1. An fara kada kuri'a a Osogbo

    An fara kada kuri'a a karamar hukumar Osogbo ne da misalin karfe takwas da minti biyar.

  2. An fito sosai

    Mutane sun fito sosai domin kada kuri'u a rumfunar zabe bakwai din da ake zaben a yau.

  3. Masu zabe suna duba sunayensu a rijista

  4. Barka da shigowa

    Jama'a, barkanku da shigowa wannan shafi inda za mu kawo muku yadda ake karasa zaben gwamnan jihar Osun da aka fara ranar Asabar.

    Ranar Lahadi ne dai hukumar zabe ta INEC ta yanke hukuncin cewar ba a kammala zaben ba, kuma za a karasa zabe a wasu rumfunar zabe bakwai da ba a yi zabe ba ko kuma aka soke zabensu.