Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 25/09/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 25/09/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Haruna Kakangi da Aisha Babangida

  1. MDD na cikin haɗari idan ba ta sauya salo ba - Tinubu

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga Majalisar Dinkin Duniya da ta canza salo idan har tana son ci gaba da kasancewa mai tasiri a duniya.

    Tinubu ya bayyana hakan ne a jawabin da ya gabatar ta hannun mataimakinsa, Kashim Shettima, a yayin taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 80 a birnin New York, inda ya zargi MDD da yin watsi da ainihin matsalolin da duniya ke fuskanta.

    A cewarsa, rashin sauya salo na iya sa duniya ta fara kauce wa Majalisar wajen tattauna muhimman lamurra.

    Shugaban ya nuna damuwa kan yadda ake tafiyar da harkokin MDD da kuma jinkirin da ake samu wajen kawo Ƙarshen rikice-rikicen kasa da kasa, musamman rikicin Falasɗinu.

    Ya ce "Rashin tsayin daka wajen ɗaukar mataki akan irin wadannan rikice-rikice ya zama babbar matsala ga rayuwar mutane” Shugaban ya jaddada cewa mafita ta dindindin ga Falasdinu ita ce tsarin kafa ƙasashe biyu domin tabbatar da zaman lafiya.

    Shugaban ya kuma sake jaddada buƙatar Najeriya ta samu kujerar dindindin a kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, yana mai cewa dole a sabunta tsarin domin ya dace da halin da duniya take ciki a yanzu.

    A bangaren tattalin arziki kuwa, Shettima ya buƙaci a samar da wata kotu ta kasa da kasa da za ta rika kula da lamuran bashi, domin taimaka wa ƙasashe masu tasowa.

  2. Ukraine da Syria sun farfaɗo da huldar jakadanci bayan shekaru na taƙaddama

    Ukraine da Syria sun dawo da huldar jakadanci a tsakaninsu a hukumance bayan shugabannin ƙasashen sun yi wata ganawa a keɓe a birnin New York a yayin babban taron Majalisar Dinkin Duniya.

    Da ya ke maraba da wannan mataki, shugaba Zelensky na Ukraine ya ce ya tattauna akan irin barazanar tsaron da ƙasashen biyu ke fuskanta tare da shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa.

    Ukraine ta dakatar da alaƙa tsakaninta da Syria ne a shekarar 2022, bayan da gwamnatin tsohon shugaban Syria Bashar al--Assad ta amince da irin mamayar da Rasha ta yi wa wasu yankuna nata.

  3. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake saduwa a shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa a hantsin Alhamis.

    Shafin na yau zai fi mayar da hankali ne kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta, da kuma sauran sassa na duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo.

    Ku kasance da mu.