Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 03/11/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Litinin 03/11/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. 'Najeriya na maraba da taimakon Amurka idan za a kare martabarta'

    Gwamnatin Najeriya ta ce za ta yi maraba da duk wani taimaka daga Amurka kan magance masatsalar masu tayar da ƙayar baya, matsawar za a mutunta kimarta.

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ambato ɗaya daga cikin masu magana da yawon shugaban ƙasar,Daniel Bwala ya fitar a ranar Lahadi ya ce ''Muna maraba da taimakaon Amurka wajen yaƙi da masu tayar da ƙaya baya a ƙasarmu matsawar za ta kare mutuncinmu''.

    Shugaba Trump na Amurka ya yi barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya, idan hukumomin ƙasar ba su ɗauki mataki bakan abin da ya kira ''yi wa kiristoci kisan kiyashi a ƙasar''.

    A ranar Lahadi ne Donald Trump ya shaida wa manema labarai cewa sojojin Amurka za su aika dakaru Najeriya ko su ƙaddamar da hare-hare ta sama domin dakatar da abin da ya kira ''kisan kiristoci a ƙasar'', sai dai bai bayar da cikakken bayani ba.

  2. SDP ta buƙaci Trump ya bai wa Najeriya tallafin soji maimakon kai hari

    Jam'iyyar SDP a Najeriya ta gargaɗi shugaban Amurka, Donald Trump da yunƙurin auka wa Najeriya.

    Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam'iyyar, Rufus Aiyenigba ya fitar - kamar yadda Jaridar Punch ta wallafa - ya buƙaci Amurka ta tallafa wa Najeriya da sojoji da bayanan sirri idan da gaske take ta damu da kashe-kashen da ke faruwa a ƙasar.

    Gargaɗin na zuwa ne bayan da Shugaba Trump na Amurka ya yi barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya idan ta kasa magance abin da ya kira 'kisan kiyashi kan kiristoci'

    Barazanar Trump ɗin ta haifar da zazzafar muhawara da ruɗani a cikin ƙasar.

  3. Gumi ya buƙaci Najeriya ta yanke alaƙa da Amurka

    Fitaccen malamin Addinin Musuluncin nan na Najeriya, Sheikh Ahmad Mahmud Gumi ya buƙaci shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya ɗauki tsattsauran mataki kan Amurka saboda barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, malamin ya soki barazanar Trump ɗin da cewa cin zarafi ne da keta alfarmar Najeriya.

    “Barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya da Trump ya yi, tsantsar raini ne ga hukumomin Najeriya, amma za mu iya dakatar da shi,'' kamar yadda ya wallafa.

    Sheikh Gumi ya shawarci gwamnatin Najeriya ta gayaci jakadan Amurka domin ta buƙaci Amurka ta janye barazanar, yana mai cewa ƙin yin hakan zai iya haifar da lalacewar dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

  4. Trump ya nanata aniyarsa ta iya ƙaddamar da hari a Najeriya

    Donald Trump ya jaddada cewa Amurka za ta iya tura dakaru Najeriya ko kuma kaddamar da hare-hare domin hana abin ya kira kisan Kiristoci da ake yi.

    Ya shaida wa manema labarai cewa ba zai bari a ci gaba da kisan ba.

    "Ana kashe kiristoci da dama a Najeriya kuma adadi da yawa, ba zan bari a ci gaba ba." in ji Trump.

    Fadar gwamnatin Najeriya ta ce za ta yi maraba da samun hadin kan Amurka wajen yaƙi da mayaka masu tsattsaran ra'ayin addini tare da musanta cewa mayakan sun fi kashe kiristoci.

    A watan da ya gabata Amurka ta saka Najeriya cikin jerin kasashen da take da damuwa da su kan take ƴancin addini.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta a ranar Asabar, Mista Trump ya ce Washington na iya shiga Najeriya da ƙarfin soji don kakkaɓe abin da ya kira ƴanta'adda masu kishin Islama da ke aikata ta'asa.

  5. Aƙalla mutum 20 sun mutu a girgizar ƙasar Afghanistan

    Gwamnatin Taliban ta ce akalla mutum 20 suka mutu, sama da mutum 300 kuma suka ji rauni sakamakon girgizar ƙasa da ta abka wa arewacin Afghanistan.

    Girgizar mai karfin maki shida ta auku ne tsakiyar daren yau Litinin - kuma ta fi shafar yankin Mazar-i-Sharif.

    Iftila'in ya kuma lalata gidaje da dama haɗi da babban masallacin mabiya Shi'a .

    Girgizar ƙasa a watan Agusta a Afghanistan ta kashe sama da mutum 2,000

  6. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Haus kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Litinin.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku kasance da shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.