Ina ne 'Timbuktu Triangle' kuma me ya sa ya zama maɓoyar Boko Haram?
Kashe sojojin Najeriya sama da 22 da mayaƙan Boko Haram suka yi a ƙarshen mako a dajin Timbuktu Triangle ya ɗaga hankalin mutane, ganin yadda aka yi asarar sojoji masu yawa a lokaci guda.
Tun a ƙarshe-ƙarshen shekarar da ta gabata ne hare-haren mayaƙan Boko Haram suka fara komawa a yankin arewa maso gabas, wanda ya daɗe yana fama da matsalar tsaro, musamman rikicin Boko Haram.
A cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran shalkwatar tsaron Najeriya, Manjo Janar Edward Buba ya fitar ranar Lahadi, ya ce, an kashe sojojin ne a lokacin da suka suka ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin mayaƙan ƙungiyar da ke yankin na Timbuktu.
Wannan ya sa BBC ta yi nazari kan ina ne wannan wuri, kuma mene ne ya sa ya zama maɓoyar mayaƙan?