Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Ahmad Bawage da Aisha Ja'afaru

  1. Firaministan Serbia Milos Vučević ya sauka daga muƙaminsa

    Firaiministan Serbia Milos Vučević (Milo Vulvi) ya sauka daga muƙaminsa sakamakon zanga-zangar ƙin gwamnati, wadda aka shafe watanni ana gudanarwa bayan mutuwar mutane 15 ya yinda rumfar wata tashar jirgin ƙasa ta rikito.

    Al'amarin ya haifar da zarge-zargen cin hanci tare da buƙatar hukunta wadanda suke da hannu.

    A daren Litinin an jikkata wata 'daliba ya yin arangama tsakanin ƴan adawa da masu goyon bayan jam'iyya mai mulki a birnin Novi sad.

    Yayin da ya ke amsa tambayoyin manema labarai a birnin Belgrade, Mista Vulvi ya roƙi al'umma su kwantar da hankulansu.

    Mista Vulvi ya ce bayan abinda ya faru a Novi Sad a daraen jiya, na dauki matakin sauka daga muƙamin firaiministan Serbia, na tyi doguwar tattaunawa da shugaban ƙasa, kuma ya amince da buƙata ta, saboda gujewa rabuwar kan al'umma, 'yan siyasa sun dauki alhakin abinda ya faru kuma a shirye suke a samar da kwanciyar hankali.

  2. Ƴantawaye na daf da ƙwace iko da garin Goma na Jumhuriyar Kongo

    Ga dukkan alamu ƴan tawayen na daf da karɓe iko da muhimmin birnin Goma da ke gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango bayan rahotannin da ke cewa sun ƙwace filin saukar jirgin samansa.

    Gwamnatin Kongo dai ta dage cewa tana samun galaba yayin da ake ci gaba da gwabza faɗa a wasu sassan birnin.

    Hukumomin agaji sun ce an wawashe ma'ajiyar kayan abinci da magunguna.

    Rikicin da ake yi tsakanin ƴan tawayen M23 da sojoji da kawayenta ya sa asibitoci sun cika maƙil da inda aka yi asarar rayuka kuma rahotanni sun nuna bayyana cewa gawarwaki na zube a kan tituna a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

    Ɓacin rai kan hare-haren ƴan tawaye ya sa masu zanga-zanga sun kai farmaki ofisoshin wasu jakadancin ƙasashen waje a Kinshasa babban birnin ƙasar.

    Kiraye-kirayen neman zaman lafiya don kawo ƙarshen faɗar na ƙara ta'azzara.

    Ana zargin ƙasar Rwanda da marawa ƙungiyar Tutsi ta M23 baya a yayin da take ci gaba kai hare-hare cikin ƴan watannin nan a faɗin yankin mai arzikin ma'adinai.

    Rwanda ta sha musanta hakan akai-akai.

    Birnin Goma da ke kan iyaka da ƙasar Rwanda, muhimmin cibiyar sufuri da kasuwanci ne da ke kusa da manyan wuraren da ake haƙo ma'adanai waɗanda ke da muhimmanci wajen ƙera wayoyin hannu da makamantansu.

  3. Ƴansanda sun kama masu sayar wa ƴanbindiga da ƴan Boko Haram babura

    Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce ta samu nasarar kama gungun masu sayar wa mayaƙan Boko Haram da ƴanbindiga a Neja da Kaduna babura.

    Rundunar ta bayyana haka ne a ranar Talata a wani taron manema labarai da mataimakin babban sufeto janar na ƴansanda mai kula da shiyya ta 7, Benneth Igweh ya yi, inda ya ce sun kama gungun mutanen ne a garin Suleja da ke jihar Neja.

    Igweh ya ce an kama Shamsuddeen Yunusa mai shekara 30 da Zaharadeen Saidu mai shekara 25 da Mustapha Haruna mai shekara 22.

    Ya ce sun kama babura 22, da makullai da dama da wayoyin salula da suka ƙwace a hannun waɗanda ake zargin.

    A cewarsa, gungun matasan sun ƙware ne wajen sata da sayarwa ko bayar da hayan baburan da ɓata-gari, ciki har da waɗanda ake zargi ƴan Boko Haram ne da suke gudanar da harkokinsu a Neja da Kaduna.

    "Sun ƙware ne wajen kai baburan ga ƴaanbindiga a Neja da yankin Birnin Gwari a jihar Kaduna," in ji shi.

  4. Colombia ta aika jiragen soji domin kwaso waɗanda aka kora daga Amurka

    Jiragen saman sojojin saman Colombia biyu da aka aika zuwa Amurka domin ɗebo baƙin haure da aka kora sun sauka a Bogotá babban birnin ƙasar.

    Baƙin hauren dai sun kasance a cikin jiragen sojin Amurka da ke kan hanyar zuwa Colombia a ranar Lahadin da ta gabata, lokacin da shugaban Colombia Gustavo Petro ya hana jirgin sojin Amurka sauka, yana mai cewa ana muzgunawa waɗanda ke cikin jirgin kamar masu laifi.

    Lamarin dai ya ya nemi ya janyo yakin kasuwanci tysakanin ƙasashen biyu bayan da Donald Trump ya yi barazanar sanya harajin kashi 25 cikin 100 kan kayayyakin da Colombia ke shigarwa Amurka.

    Jami'an diflomasiyya na ƙasashen biyu sun cimma matsaya, inda Colombia ta aike da jiragenta na rundunar sojin sama domin karɓar baƙin hauren, matakin da Petro ya ce ya tabbatar da an mutunta su.

    Da alama dai yadda ake yi wa ƴan gudun hijirar da aka kora a cikin jiragen sojin Amurka ya janyo cece ku ce tsakanin gwamnatocin biyu.

    Colombia ta amince da fitar da karɓar jiragen baƙin haure daga Amurka a baya: a shekarar 2024, jirage 124 ɗauke da baƙin haure daga Amurka sun sauka a ƙasar.

  5. 'Asibitoci sun cika da ɗaruruwan waɗanda suka samu raunuka a Goma'

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce asibitoci sun cika maƙil da 'daruruwan majinyata da suka samu raunuka a gabashin Goma, inda ƴan tawayen M23 da Ruwanda ke goyon baya suke yunƙurin ƙwace birnin daga sojojin Congo.

    Akwai gawarwaki da dama kan tituna ya yinda ake ci gaba da fafata yaƙi, Majalisar Dinkin Duniya ta ce an samu rahotannin yadda mayaƙan suka aikata fyade.

    Dr Adelheid Marschang babbar jami'ar Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce WHO ta damu musamman da lafiya da tsaron mata da ƴan mata da masu juna biyu wadanda ke cikin hatsari, dama akwai yawaitar mutuwar masu juna biyu ya yin haihuwa tun kafin ɓallewar rikicin.

    Hukumar Lafiya ta Duniya na aiki tare da hukumomi da abokan hulda don neman mafita.

  6. Jami'an Rasha sun isa Syria don tattaunawa da sabon gwamnatin

    Kafar yaɗa labaran Rasha ta ce jami'an Moscow da suka ziyarci Siriya a karon farko bayan hamɓarar da gwamnatin Bashar al-Assad sun isa Damascus.

    Ana sa ran membobin tawagar za su gana da sabon shugaban Siriya.

    Fatan da Rasha take yi na barin sansanin sojinta a Tartous da Latakia na sahun gaba cikin batutuwan da taron zai mayar da hankali.

    Rasha wadda ta taimakawa Assad da sojoji wajen zaman sa a mulki ya yin yakin basasa ta ba shi mafaka a watan disamba.

  7. Masar ta ƙaryata cewar Al-Sisi ya tattauna da Trump

    Masar ta ƙaryata cewar shugaban ƙasar Abdel Fattah al-Sisi ya yi magana da shugaba Trump, tun bayan da shugaban Amurka ya yi kiran a mayar da sama da Falasɗinawa miliyan ɗaya daga Gaza zuwa Masar da sauran ƙasashen Larabawa.

    A ranar Litinin Mista Trump ya bayyana cewar zai yi magana da shugaban Masar ta wayar tarho kuma ya na fatan zai amince ya karɓi wasu Falasdinawan.

    Kafar yaɗa labaran Masar ta ce ɓangarorin biyu basu yi magana da juna ba, bugu da ƙari ƙasar ta yi Allah wadai da abinda ta kira cin zarafi ga Falasdinawa da kuma tauye haƙƙin ƙasarsu.

  8. Rundunar ƴan sandan Abuja ta tarbi sababbin jami'ai 112

    Rundunar ƴan sandan Najeriya reshen birnin Abuja ta karɓi sabbin ƴan sanda 112 waɗanda aka yaye a baya bayanan daga makarantar horar da ƴan sanda da ke jihar Neja.

    Da yake karɓarsu, kwamishinan ƴan sandan Abuja, Olatunji Disu ya bayyana cewa ƙarin ƴan sandan ba shakka zai taimaka wa rundunar a aikinta na tabbatar da tsaro da zaman lafiya a faɗin birnin.

    Kwamshinan ƴan sandan ya kuma buƙaci sabbin jami'an su yi aiki cikin ƙwarewa, da gaskiya da mutunci.

    Ƴan sandan na cikin ƴan sanda 10,000 da suka samu nasarar kammala samun horo a makarantar horar da ƴan sanda a ranar 23 ga watan Janairun 2025.

  9. Hannun jarin kamfanonin haɗa na’aurori na ci gaba da faɗuwa a kasuwannin Asia

    Farashin hannun jarin kamfanonin haɗa na’aurori na ci gaba da faɗuwa a kasuwannin nahiyar Asia, bayan da hannun jarin kamfanin haɗa ƙwaƙwalwar kwamfuta na Amurka, Nvidia ya yi asara mafi girma a tarihinsa a kasuwar hannun jari ta Amurkar.

    A Japan, wani kamfani da ke samar wa Nvidia da kaya ya yi ƙasa da kashi 10 cikin ɗari, yayin da kamfanin Softbank ya faɗi da kashi shida cikin ɗari.

    Wannan asarar da kamfanonin suka tafka na zuwa ne bayan sakin ƙirƙirarriyar basirar Matambayi ta DeepSeek mai matuƙar arha, mallakin wani kamfanin ƙasar China.

    Wannan ya sauya tunanin da ake da shi kan kuɗin da za a kashe ko ƙarfin lantarki da ake buƙata wajen samar da irin wannan fasaha, idan har China za ta iya samar da ita ta amfani da abubuwa ƴan ƙalilan.

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ya kamata wannan ya zamo matashiya ga kamfanonin fasahar zamani na Amurka.

  10. Faransa ta yi Alla-wadai da far wa ofishin jakadancinta a Kinshasa

    Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Noel Barrot ya yi Alla-wadai da far wa ofishin jakadancin ƙasar a Kinshasa - wanda masu zanga-zanga suka yi a safiyar yau Talata.

    "Ba za mu lamunci irin waɗannan hare-hare ba," kamar yadda ya faɗa a shafin X, inda ya ƙara da cewa masu zanga-zanga "sun haddasa wutar da yanzu a shawo kanta".

    An ga hayaki na tashi sama daga ofshin jakadancin, bayan cinna wa wani ɓangarensa wuta.

    "Muna yin duk abin da ya kamata domin kare lafiyar wakilai da kuma ƴan ƙasar mu," in ji Barrot.

    Masu zanga-zanga sun kuma far wa ofisoshin jakadancin ƙasashen Rwanda da Uganda da Belgium da Netherlands da kuma Amurka.

  11. Sojoji sun ƙwato tarin makamai a Zamfara, suna cigaba da neman Bello Turji

    Dakarun Operation Fansan Yamma tare da haɗin gwiwar jami'an tsaron farin kaya (DSS), sun ce sun ƙwace tarin makamai a karamar hukumar Kauran Namoda na jihar Zamfara.

    Dakarun sun kai samamen ne bayan samun bayanan sirri kan masu safarar makamai daga Jamhuriyar Nijar zuwa Najeriya.

    Wata sanarwa da jami'in yaɗa labaran rundunar Laftanar-Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, ya ce sun kaddamar da farmaki ranar 27 ga watan Janairun 2025, abin da ya kai ga ƙwato makaman kan hanyar Namoda zuwa Zurmi.

    Ya ce waɗanda ake zargin sun tsere zuwa cikin daji tare da barin motarsu bayan artabu da sojoji.

    Kanal Abubakar ya ce bayan bincike da suka yi a cikin motar, sun gano makamai da dama da suka haɗa da bindigar AK-47 guda tara da harsasai daban-daban.

    A ɗaya gefen, dakarun sun ce suna cigaba da neman inda Bello Turji yake wanda ake nema ruwa a-jallo - wanda yake cigaba da tserewa sojoji ta hanyar guduwa daga maɓoya zuwa maɓoya.

    Dakarun sun tabbatar da cewa suna aiki tukuru domin kama Turji domin mayar da zaman lafiya a al'ummomin da suka addaba da hare-hare.

  12. Neymar na daf da komawa Santos bayan barin Al-Hilal

    Ƙungiyar kwallon kafa ta Santos da ke Brazil na tattaunawa da Neymar domin sake ɗaukar ɗan wasan bayan amincewa da kawo karshen yarjejeniyarsa da Al-Hilal ta Saudiyya.

    Ana sa ran ɗan wasan na Brazil mai shekara 32 zai saka hannu kan yarjejeniya ta ƙankanin lokaci da ƙungiyar - wadda a nan ne ya fara rayuwarsa ta tamaula.

    Kawo karshen yarjejeniyar da Al-Hilal wani babban mataki ne da Neymar ya ɗauka, a cewar majiyoyi kusa da shi.

  13. Hotunan yadda ɗaruruwan ƴan gudun hijira ke kwarara zuwa Rwanda daga Goma

    Hotunan sun ɗaruruwan ƴan gudun hijira na ta kwarara zuwa garin Gisenyi na Rwanda daga birnin Goma.

    "harsasai daga artabu da ake yi na ta faɗuwa kusa da mu, ɗaya ya faɗi a kan gidan makwabcina tare da hallaka ta da ƴaƴanta shida, lokacin ne na yanke shawarar tserewa", kamar yadda Jeanne Karuba ta shaida wa BBC bayan da ta tsallaka iyaka zuwa Rwanda riƙe da ɗanta guda da kuma wasu kayaki a kanta.

    Ta ki amincewa a ɗauki hotonta inda ta ce ba ta ci komai ba cikin kwanaki da suka gabata, tare da cewa me ya sa za ku ɗauke ni ba tare da kun ba ni abinci ba?"

  14. Fadar Sarkin Musulmi ta ce Laraba za a fara duba watan Sha'aban

    Fadar Sarkin Musulmi a Najeriya Mai Alfarma Sa'ad Abubakar III ta buƙaci al'ummar Musulmi da su fara duba sabon watan Sha'aban na kalandar musulunci daga daren Laraba.

    Kwamitin ganin wata na Najeriya a fadar Sarkin Musulmi ya ce ranar Lahadi ce za ta zama 29 ga watan Rajab daidai da 29 ga watan Janairun 2025.

    Wata sanarwa da fadar Sarkin Musulmin ta fitar, ta ce idan aka ga watan a kai rahoto zuwa ga hakimi ko kuma ma unguwa mafi kusa wanda shi kuma zai sanar da fadar.

    Watan Sha'aban dai yana da muhimmanci a kalandar Musulunci, saboda daga shi ne za a shiga watan azumin Ramadan.

  15. An fara gangamin goyon bayan ficewar Nijar daga ECOWAS

    Ana can ana gudanar da wani gangami domin nuna goyon bayan ficewar Nijar daga ƙungiyar ECOWAS ko CEDEAO.

    Ƙungiyoyi daban-daban ne suka fito a Yamai, babban birnin ƙasar don yin gangamin.

    Wakiliyar BBC ta ruwaito cewa irin wannan gangami yana can yana gudana a sauran yankunan ƙasar.

    Masu da’awar kishin ƙasa da dama ne suka fito tare da magoya bayansu domin nuna goyon baya ga shugabanin ƙasashen AES da kuma adawa ga c gaba da amfani da kuɗin CFA a cikin ƙasashen uku na kungiyar da suka haɗa da Nijar da Mali da kuma Burkina Faso.

  16. Yadda zamani ke yi wa majemar Kano barazana

  17. Gwamnatin Kongo ta ce sojojinta ne ke iko da mafi yawan unguwannin Goma

    Wani jami’in gwamnati a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ya sanar da cewa yanzu haka sojojin ƙasar ne ke iko da mafi yawan unguwannin birnin Goma, da ke gabashin ƙasar.

    Muhingo Nzangi, wanda shi ne ɗan majalisa mai wakiltar yankin ya shaida wa ƴan jarida cewa sojojin sun yi maganin ƴan tawayen M23 waɗanda MDD ta ce na samun goyon bayan Rwanda.

    Sai dai har yanzu ƴan tawayen na iƙirarin cewa suna iko da birnin.

    Wakiliyar BBC ta ce M23 na ikirarin cewa tana kokarin kare tsirarun ƴan ƙabilar Hutu ne waɗanda ake ci wa zarafi, kuma wannan lamari ne da Rwanda take goyon baya, sai dai ta ce ba ta tsoma hannu kai-tsaye cikin rikicin ba duk kuwa da cewa Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce tana da hannu.

    Tuni dai Amurka ta yi Alla-wadai da harin da aka kai kan birnin.

  18. An tasa ƙeyar ɗan Najeriya zuwa Amurka kan zargin amfani da hotunan tsiraici

    An tasa ƙeyar wani ɗan Najeriya zuwa Amurka domin fuskantar tuhuma kan zargin amfani da hotunan tsiraici domin tatsar kuɗi kan yaro bature, lamarin da ya kai ga yaron ya kashe kansa.

    Dan Najeriyar, Hassan bin Hussein Abore Lawal ya kasance yana bayyana kansa a matsayin budurwa a shafukan sada zumunta, inda ya yi amfani da hakan wajen yaudarar yaron mai suna Gavin Guffey, wanda ya riƙa turo masa hotunan tsiraici.

    Daga baya Hassan ya yi barazanar yaɗa hotunan idan yaron mai shekara 17 bai tura masa kuɗi ba.

    Yanzu haka Lawal, mai shekara 24 a duniya na iya fuskantar hukuncin ɗaurin rai-da-rai idan aka tabbatar da laifin nasa.

  19. Falasɗinawa sama da rabin miliyan ne za su koma gida a yau Talata

    Ana sa ran cewa Falasɗinawa sama da rabin miliyan za su koma gidajensu a arewacin Gaza a yau Talata.

    Ƙungiyar Hamas ta ce sama da Falasɗinawa dubu 300 waɗanda yaƙi ya tarwatsa sun koma gidajensu da aka yi raga-raga da su a arewacin Gaza a ranar Litinin.

    Hotunan da aka gani a yau sun nuna yadda Falasɗinawan ke tafiya a cikin motoci suna ratsa yankunan da aka yi wa rugu-rugu, sannan har yanzu akwai waɗanda suke taka sayyada a ƙoƙarinsu na komawa gida.

    Ƙungiyar Islamic Jihad ta saki bidiyon da ke nuna cewa ɗaya daga cikin waɗanda za a saki, Abel Yehud, na nan a raye, wadda ake taƙaddama kan sakin ta tsakanin ɓangarorin biyu.

    Isra’ila ta ce ta tabbatar cewa takwas daga cikin waɗanda aka tsara cewa Hamas za ta saki ƙarƙashin yarjejeinyar tsagaita wuta, sun mutu.

  20. Neymar ya raba-gari da Al-Hilal ta Saudiyya

    Ƙungiyar Al-Hilal ta Saudiyya da ɗan wasan Brazil Neymar sun amince su kawo ƙarshen kwantaragin ɗan wasan.

    Neymar, mai shekara 32 a duniya ɗan asalin ƙasar Brazil ya je Al-Hilal ne a watan Agustan shekarar 2023 kan kuɗi Yuro miliyan 90, sai dai sau bakwai kacal ya buga wa ƙungiyar wasa sanadiyyar rauni da ya addabe shi.

    A kakar da ke ci sau biyu kawai Neymar ya buga wasa, na baya-bayan shi ne lokacin da aka yi canji da shi a watan Nuwamba.

    Ana alaƙanta shi da komawa ƙungiyarsa ta asali, wato Santos, da ke Brazil.

    "Ƙungiyar ta gode wa Neymar kan gudumawar da ya bayar a lokacin zaman shi a Al-Hilal, kuma tana masa fatan alkhairi a nan gaba," in ji ƙungiyar.