Aljeriya da Mali sun dakatar da jirage sauka a ƙasashen juna
Ƙasashen Aljeriya a Mali sun dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a tsakaninsu yayin da rikicin difilomasiyya ke ci gaba da ruruwa tsakanin ƙasashen na Sahel.
A ranar Lahadi Mali ta zargi maƙociyar tata da ɗaukar nauyin ta'addanci, ba tare da bayar da wata hujja ba, bayan Aljeriyar ta harbo jirgin Mali maras matuƙi a makon jiya.
Aljeriya ce ta fara dakatar da saukar jirage daga Mali, inda daga baya ita ma ta ce ta ɗauki matakin kan dukkan jiragen da ke fitowa daga Aljeriya.
Aljeriya ta ce jirgin ya keta alfarmar sararin samaniyarta, abin da Mali ta musanta da kakkausar murya.
Mali ta ce harbo jirgin "aikin tsokana ne". Ita kuwa Aljeriya ta ce zargin ɗaukar nauyin ta'addanci "abin dariya ne...da ba shi buƙatar amsa".