Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 21/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 21/06/2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Jam'iyyar Gwamnati a Ethiopia na kan gaba a zaɓen ƙasar

    Jam'iyyar Firaministan Habasha Abiy Ahmed ta lashe zaɓen ƙasar da gagarumin rinjaye.

    Hukumar zaɓen ƙasar ta ce jam'iyyar ta samu kujerun majalisar dokoki 438 daga cikin 540 da aka zaɓa.

    Jam'iyyar ta doke ƴan adawa a zaɓen, wanda aka gudanar cikin yanayin fargaba da ƙorafi daga ƴan adawar.

  2. An ci gaba da zaɓen zagaye na biyu a Colombia

    Al'ummar Colombia na kaɗa ƙuri'a a zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasar.

    Ana hasashen ƙuri'ar ta yi kyau ga sabon shigar siyasa, kuma mai tsattsauran ra'ayi wanda ke fatan amfani da ƙarfi wajen yaƙi da ƙungiyoyin safarar ƙwaya da na ƴan tawaye.

    Abelardo de-la-Espriella, ya yi alƙawarin amfani da ƙarfin soji wajen murƙushe duk masu barazana ga zaman lafiyar ƙasar.

    Abokin karawarsa Sanata Ivan Cepeda mai sassaucin ra'ayi, yana fatan ɗorawa kan tsare-tsaren shugaba mai barin gado, Gustavo Petro.

  3. Save The Children ta ƙaddamar da dabarun nusar da yara game da Ebola a DR Kongo

    Ƙungiyar Agaji ta Save The Children ta ƙaddamar da wani shiri na koyar da ƙananan yara dabarun kauce wa kamuwa da Cutar Ebola da guje wa labaran ƙarya game da cutar a makarantun Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo.

    Shirin wanda zai ƙunshi dabarun wasanni wajen koyar da yara, za a gudanar da shi a ɗaukacin makarantun ƙasar, domin wayar da kan ƙananan yara game da illolin cutar da kuma hatsarinta.

    Shirin na Save The Children, wanda ya ƙunshi dabarun amfani da kayan wasan yara da waƙe-waƙe an ƙaddamar da shi ne domin nusar da yaran game da illar cutar da ke ci gaba da yi wa Jamhuriyar Dimokraɗiyyar kongo barazana.

    Fargaba da labaran ƙarya game da cutar sun sa ana far wa jami'an lafiya da cibiyoyin kula da masu ɗauke da cutar da kuma rage zuwa makaranta a wasu sassan ƙasar, a cewar ƙungiyar.

    Yayin da ke ake ci gaba da jarrabawar ƙarshen zangon karatu a faɗin ƙasar, Save The Children ta ƙaddamar da sabbin dabaru ga malamai da kuma ɗaliban domin kare yaɗuwar cutar ta Ebola a makarantu.

    A wani ɓangare na shirin ƙungiyar ta samar wa makarantu 33 kayayyakin gwajin cutar da abubuwan da ke taimakawa wajen yaƙi da ita, kamar na'urorin wanke hannu da abubuwan tsafta.

    Malaman makaranta a ƙasar na cewa fargaba tsakanin ɗalibai da kuma yaɗuwar labaran ƙarya tsakanin mutane game da cutar na ci gaba da bazuwa tare da haifar da tsoro, lamarin da ke kawo koma-baya a harkar koyo da koyarwa.

    Zuwa yanzu dai cutar Ebola ta kashe mutum 232 ciki har da ƙananan yara 26 tun bayan sake ɓarkewarta a ƙasar, kamar yadda hukumar lafiyar ƙasar ta bayyana.

    Save The Children ta shafe fiye da shekara 30 tana aiki da ƙungiyoyi da hukumomin Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo wajen tallafa wa ƙasar a fannoni daban-daban da suka haɗa da na lafiya da abinci mai gina jiki da ilimi da ruwan sha da tsaftar muhalli da sauransu.

  4. An fara jarjejeniyar zaman lafiya ta dogon zango tsakanin Iran da Amurka

    An gudanar da kashin farko na tattaunawar yarjejeniyar zaman lafiya mai dogon zango tsakanin Amurka da Iran.

    Yayin da ya bayyana zaman da na tarihi, mataimakin shugaban Amurka, JD Vance ya ce an samu gagarumin ci gaba a tattaunawar.

    To amma kafofin yaɗa labaran Iran na bayar da rahoton cewa wakilan ƙasar sun ƙi wallafa hoton ganawar da aka kwashe mintuna 80 ana yi.

    Haka kuma bayanai sun ce wakilan na Iran sun fusata da sabon barazanar Trump na yi wa Iran ruwan bama-bama idan ta kasa dakatar da mayaƙan Hezbollah da ke goyon baya a Lebanon.

    Babban mai shiga tsakani na ƙasar, Mohammad Bagher Ghalibaf ya gargaɗi Amurka ta shiga taitayinta.

    Rahotonni na cewa Tehran ta ƙi yarda a tattauna batun nukiliyarta har sa Isra'ila ta dakatar da hare-harenta a Lebanon.

  5. Yadda za ku kula da cibiyar sabbin jarirai kafin ta faɗi

    Ana yanke cibiyar jariri da zarar an haife shi, domin ba ta da sauran amfani.

    Domin da ta daina samun jini sai ta fara bushewa ta yi tauri, a cewar shafin intanet na gidauniyar NHS reshen asibitin jami'ar Milton Kyenes.

    Sai dai kafin ta kai ga faɗuwa, akwai wasu shawarwari kan yadda ya kamata a kula da cibiyar sabon jariri.

    Abu mafi matuƙar muhimmanci shi ne wanke hannu a kodayaushe a yayin kulawa da jariri.

    Haka kuma kada a dinga taɓa cibiyar da hannu domin kauce wa sanya wa jariri ƙwayoyin cuta, a kuma kiyaye sanya wa jariri matsattsun kaya domin cibiyar ta dinga shan iska.

    Haka zalika asibitin ya bayar da shawarar kada a cire abin da aka maƙale cibiyar da shi saboda nauyinsa na taimaka wa wajen faɗuwar cibiyar jariri.

  6. Masu iƙirarin jihadi sun kashe manoma 11 a Borno

    AƘalla mutum 11 aka bayar da rahoton masu iƙirarin jihadi sun kashe a wasu ƙauyukan jihar Borno da ke arewacin Najeriya a ranar Asabar.

    Wata ƙungiya mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi a jihar Borno ta ce an kashe wasu manoma bakwai a yayin da suke shuka a gonakinsu.

    Haka ma rahotonni sun ce an kashe wasu manoman huɗu a yankin tafkin Chadi.

    Asusun bayar da lamuni na duniya ya yi gargaɗin cewa rikicin zai iya durƙusar da harkokin noma, lamarin da ka iya ƙara yaɗuwar talauci tsakanin al'umomin yankin.

  7. Isra'ila ta dage cewa sojojinta za su ci gaba da mamaye kudancin Lebanon

    Isra'ila ta dage cewa sojojinta za su ci gaba da mamaye kudancin Lebanon - saɓanin abin da Iran ke buƙata na su janye a wani ɓangare na yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙi da ta cimma da Amurka.

    Ministan tsaron ƙasar, Israel Katz, ya ce dakarun ƙasarsa za su ci gaba da tsayawa domin kare arewacin Isra'ila daga harin Hezbollah.

    Cikin wani saƙo da Shugaba Trump ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, ya yi barazanar sake far wa Iran da ''ƙarfi'' idan har ba ta dakatar da dakarun da take goyon bayansu a Lebonon ba.

  8. Ƙasashen 4 na son yarjejeniya mai ɗorewa tsakanin Iran da Amurka

    Ministocin harkokin wajen ƙasashen Pakistan da Turkiyya da Saudiyya da Masar sun buƙaci a samu yarjejeniya mai ɗorewa kuma tabbatacciya tsakanin Iran da Amurka.

    A yayin wani taro da suka yi a birnin Alƙahira, ministocin sun kuma yi kira da a hanzarta cigaba a tattaunawar da ke gudana tsakanin ƙasashen biyu a Switzerland.

    A cikin sanarwar haɗin gwiwar da suka fitar, sun ce ya kamata a cimma matsaya wadda za ta kasance amintacciya, mai ɗorewa, kuma karɓaɓɓiya ga ɓangarorin biyu.

    Sun ƙara da cewa dole ne yarjejeniyar ta yi la’akari da damuwar yankin, musamman batun tsaro da zaman lafiya a ƙasashen yankin Tekun Fasha.

  9. Dole ne Iran ta dakatar da dakarun da take mara wa baya a Lebanon - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya jaddada cewa dole ne Iran ta dakatar da dakarun da take mara wa Lebanon baya nan take, yana gargadin cewa idan ba ta yi hakan ba, Amurka za ta sake kai mata hari mai tsanani fiye da wanda aka kai a makon da ya gabata.

    Trump ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, jim kaɗan bayan kalaman mataimakinsa J.D. Vance gabanin taron ƙasashe huɗu da aka gudanar a Switzerland.

    Ya ce, dole ne Iran ta gaggauta dakatar da waɗannan dakarun da take tallafawa da kuɗi masu yawa, yana mai cewa suna haddasa rikici a Lebanon.

    A halin yanzu kuwa, ana ci gaba da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka a ƙasar Switzerland, inda kuma ƙasashen Qatar da Pakistan ke halarta domin lalubo mafita kan takaddamar da ke tsakaninsu.

  10. Za a ba mu dala biliyan 12 a zango biyu - Iran

    Ministan harkokin tattalin arziki da kuɗi na Iran, Ali Madanizadeh, ya bayyana cewa za a saki dala biliyan 12 ga ƙasar a zango biyu bayan aiwatar da yarjejeniyar da ƙasar ta cimma da Amurka, inda za a fara sakin dala biliyan 6, sannan daga baya a sake sakin wani biliyan 6 kamar yadda yarjejeniyar ta tanada.

    Madanizadeh ya ce bisa sashe na 11 na takardar yarjejeniyar, Amurka ta ɗauki alƙawarin ba Iran cikakken damar amfani da kadarorinta da aka ƙwace ciki har da kuɗaɗen waje da aka tara.

    Ministan ya kuma jaddada cewa waɗannan kuɗade na da alaƙa da kuɗaɗen man fetur na shekarun baya, kuma zancen cewa dole ne a kashe su ne wajen sayen kayayyakin Amurka kawai, jita-jita ce marar tushe, yana mai cewa za a ƙara fayyace yadda za a saki kuɗaɗen yayin tattaunawa.

  11. An fara tattaunawar Iran da Amurka a Switzerland

    An fara tattaunawar Iran da Amurka a ƙasar Switzerland tare da halartar masu shiga tsakani daga Qatar da Pakistan.

    Rahotanni sun ce an fara zaman ne a katafaren wurin taro na Bürgenstock, inda wakilai daga ɓangarorin ke ƙoƙarin ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma a baya

    A cewar bayanai, batutuwan da za su fi mayar da hankali a kai sun haɗa da tsagaita wuta a Lebanon da kuma sakin kudaden Iran da aka ƙwace a ƙasashen waje.

    Ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta kuma tabbatar da cewa an fara tattaunawar tsakanin Iran da Amurka tana mai fatan za a cimma yarjejeniya mai dorewa.

  12. Su waye ke cikin tawagar Iran a tattaunawar sulhu a Switzerland?

    Tawagar Iran da za ta shiga tattaunawa da Amurka ta isa filin jirgin sama na Zurich a Switzerland daren Asabar, kafin ta wuce otel ɗin Bürgenstock inda ake gudanar da zaman.

    Shugaban tawagar shi ne Kakakin Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, yayin da Ministan Harkokin Waje, Abbas Araqchi, shi ne babban jami’in diflomasiyya mafi girma a cikin tawagar.

    Sauran manyan jami’an da ke cikin tawagar sun haɗa da Ali Bagheri, mataimakin harkokin ƙasashen waje a Majalisar Tsaron Ƙasa, da Kazem Gharibabadi, mataimakin ministan harkokin waje mai kula da shari’a da hulɗar ƙasa da ƙasa.

    Haka kuma akwai Esmail Baghaei, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran.

    Baya ga ‘yan siyasa da jami’an diflomasiyya, akwai kuma wasu manyan jami’an tattalin arziki cikin tawagar, ciki har da gwamnan Babban Bankin Iran Abdolnaser Hemmati, da Hamid Bord, mataimakin ministan man fetur kuma shugaban kamfanin mai na ƙasa.

  13. Za a fi mayar da hankali kan batun tsagaita wuta a Lebanon a tattaunawarmu da Amurka - Iran

    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya ce batun tsagaita wuta a Lebanon shi ne za a fi mayar da hankali a kai kuma zai fi ɗaukar hankali a tattaunawar da za a yi tsakanin Iran da Amurka a Switzerland.

    Baghaei ya bayyana haka ne a gab da fara tattaunawar, inda ya zargi Amurka da kasa tabbatar da tsagaita wuta a Lebanon, yana mai cewa wannan batu zai zama muhimmin abin da za a tattauna.

    Ya kuma ce Amurka, a matsayinta na abokin tattaunawa, tana da alhakin tilasta Isra’ila dakatar da hare-haren da take kai wa Lebanon.

    A cewarsa, Iran ta riga ta cika nauyin da ke kanta na yarjejeniyar, yana mai jaddada cewa kowane ɓangare ya kamata ya bi alkawuran da aka ɗauka.

  14. 'Za a yi taron ɓangarori huɗu tsakanin Iran, Amurka, Qatar da Pakistan'

    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya ce an tsara gudanar da taron ɓangarori huɗu tsakanin Iran, Amurka, Qatar da Pakistan a yau a katafaren wurin taro na Bürgenstock da ke Switzerland.

    Baghaei ya shaida wa kafafen yaɗa labarai na ƙasa cewa za a fara da ganawa tsakanin Iran da masu shiga tsakani, wato Qatar da Pakistan, kafin a ci gaba da taron haɗin gwiwar.

    Ya ƙara da cewa wannan taro wani ɓangare ne na aiwatar da yarjejeniyar da Iran da Amurka suka rattaba wa hannu a wannan mako, domin ci gaba da matakan sulhu tsakanin ɓangarorin biyu.

  15. Araqchi ya gana da ministan harkokin wajen Switzerland a wajen tattaunawar Iran da Amurka

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, ya gana da takwaransa na Switzerland, Ignazio Cassis, a otel ɗin Bürgenstock inda ake gudanar da tattaunawar Iran da Amurka.

    Ganawar ta kasance ta farko cikin shirye-shiryen hukuma na tawagar Iran a Switzerland, kuma an yi ta ne a gefen tattaunawar, inda ta ɗauki kusan mintuna 45.

    Ana sa ran a yau tawagogi daga Iran da Amurka, tare da masu shiga tsakani daga Pakistan da Qatar, za su gudanar da taron haɗaka na ɓangarori huɗu domin ci gaba da tattaunawar sulhu.

    Kafin wannan, an tsara fara ganawa ta ɓangare biyu tsakanin Iran da wakilan Pakistan da Qatar, kafin daga bisani a haɗa dukkan ɓangarorin a taro guda.

    Sai dai har yanzu ba a bayyana cikakken jadawalin tattaunawar ko yadda za ta gudana ba.

  16. Firaministan Pakistan ya isa Switzerland kan tattaunawar Iran da Amurka

    Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif, ya isa ƙasar Switzerland domin halartar tattaunawar da ake yi tsakanin Iran da Amurka, kamar yadda ofishinsa ya sanar.

    Shugaban Rundunar Sojin Pakistan, Field Marshal Asim Munir, na tare da shi a wannan tafiya, inda su biyun za su shiga cikin zaman tattaunawar.

    Pakistan ta kasance babbar mai shiga tsakani a tattaunawar zaman lafiya da ake yi tsakanin Iran da Amurka a ‘yan watannin da suka gabata.

    Tun da farko, Ma’aikatar Harkokin Wajen Pakistan ta bayyana cewa wakilai daga Amurka da Iran, tare da masu shiga tsakani daga Pakistan da Qatar, ne za su halarci wannan taro.

  17. ‘Amurka ta yi wa Iran tayin dala biliyan 6 don binciken nukiliyarta’

    Amurka na neman Iran ta amince da bai wa masu binciken Majalisar Ɗinkin Duniya damar duba cibiyoyin nukiliyarta, a madadin hakan kuma a ba ta damar amfani da wani ɓangare na kudaden da aka ƙwace mata, ciki har da dala biliyan 6 da ke Qatar.

    Rahoton Axios, wanda ya ambato majiyoyi guda biyu na yankin, ya ce Amurka na son a kammala zagayen farko na tattaunawa da wannan yarjejeniya wato Iran ta gayyaci masu bincike zuwa wuraren nukiliyarta.

    An bayyana cewa waɗannan cibiyoyi sun taɓa zama wuraren da Amurka da Isra’ila suka kai hare-hare a baya, kuma ba a kai irin wannan bincike ba tun watan Yuni 2025.

    A musayar wannan amincewa, Amurka na shirin ba Iran damar samun wasu daga cikin dukiyarta da aka ƙwace a ƙasashen waje, inda za a fara da asusun dala biliyan 6 da ke Qatar.

    Rahotannin sun ce za a takaita amfani da kuɗin ne ga sayen kayayyakin jin-ƙai kamar abinci da magunguna, ba tare da amfani da shi a wasu harkoki ba

    A lokaci guda, tattaunawar za ta kuma mayar da hankali kan batun shirin nukiliyar Iran da kuma ƙoƙarin cimma tsagaita wuta a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Sai dai rikicin da ke faruwa a Lebanon na barazana ga nasarar wannan shiri.

    Mataimakin Shugaban Amurka, JD Vance, ya ce wannan rikicin na iya kawo cikas ga tattaunawar.

    A baya, Isra’ila da Hezbollah sun amince da tsagaita wuta a ranar Juma’a domin kauce wa tangarɗa ga tattaunawar amma kuma Isra;ila ia keta yarjejeniyar.

  18. Oyebanji na APC ya lashe zaɓen gwamnan Ekiti

    Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Ƙasa (INEC) ta ayyana Gwamna Biodun Oyébanji a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Ekiti da aka gudanar ranar Asabar 20 ga Yuni, 2026.

    Shugabar tattara ƙuri’u, Farfesa Adenike Oládìjì, ta sanar da sakamakon da sanyin safiyar Lahadi, inda ta bayyana cewa Oyébanji na jam’iyyar APC ya samu ƙuri’u 319,224.

    Ɗan takarar jam’iyyar PDP, Wọlé Olúyẹdẹ, ne ya zo na biyu da ƙuri’u 40,543, yayin da ɗan takarar ADC, Dáré Bẹ́jìde, ya samu ƙuri’u 12,872.

    Gaba ɗaya, ‘yan takara 14 ne suka fafata a zaɓen, kuma Oyébanji ya samu nasara a dukkan ƙananan hukumomi 16 na jihar.

    A babban birnin jihar, Ado Ekiti, jam’iyyar APC ta fi ƙarfi inda Oyébanji ya samu ƙuri’u 38,026, wanda ya nuna gagarumar nasara a duk fadin jihar.

    Da wannan sakamako, Oyébanji ya sake lashe zaɓen gwamna karo na biyu, abin da ya zama tarihi a jihar saboda ba kasafai gwamnoni ke samun nasarar wa’adi biyu a jere ba tun daga kafuwar jihar a 1996.

    Bayan sanar da nasarar, gwamnan ya gode wa al’ummar jihar Ekiti, yana mai cewa wannan babbar amincewa ce daga jama’a ga aikin da gwamnatinsa ke yi.

  19. Assalamu alaikum

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye.

    Kamar kullum, yau ma za mu muku labaran abubuwan da ke faruwa game da yaƙin Iran da wasu muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a wannan rana ta Lahadi.

    Za ku iya yin tsokaci a shafukanmu na sada zumunta: Facebook, X, instagram, YouTube da kuma zaurenmu na WhatssApp.