Iran na ci gaba da luguden wuta kan Isra'ila da sansanonin sojin Amurka
Iran na ci gaba da yin luguden wuta kan Israila da sansanonin sojin Amurka a ƙasashen gabas ta tsakiya.
Saudiyya ta ce wasu jirage marasa matuƙa biyu na Iran din sun kai hari kan Ofishin Jakadancin Amurka da ke babban birnin ƙasar, Riyadh.
Ma’aikatar tsaron ƙasar ta ce ta samu nasarar kakkaɓo wasu jirage marasa matuƙa guda takwas da ke kan hanyarsu ta zuwa babban birnin, da kuma birnin Al-Kharj da ke kusa.
Ofishin Jakadancin Amurka ya bai wa ‘yan ƙasarsa da ke zaune a masarautar shawarar su nemi mafaka a inda suke.
Ƙasashen Qatar da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa da kuma Isra’ila su ma sun bayar da rahoton cewa makamai masu linzami na ta yawo a sararin samaniyarsu.
Yanzu haka Amurka ta bukaci yan kasarta da ke zaune a kasashe goma sha biyu na yankin su fice cikin gaggawa.