Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na 22 ga watan Maris 2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Nan da wata shida za a kammala ginin majalisar dokokin jihar Rivers - Ibas

    Ibok-Ete Ekwe Ibas

    Asalin hoton, Ibok-Ete Ekwe Ibas

    Shugaban gwamnatin riƙon-ƙwarya na jihar Rivers, Ibok Ibas ya ce nan da wata shida za a kammala sake gina majalisar dokokin jihar.

    Ibas ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyarar gani da ido a harabar majalisar a ranar Asabar, inda ya ce ya lura akwai buƙatar kammala ginin.

    Ya buƙaci ɗan kwangilar da ke aikin da ya ƙara ƙaimi wajen kammala ginin kamar yadda aka amaince a yarjejeniyar kwangilar, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    A cewarsa, daga cikin aikin da aka ba shi akwai tabbatar da majalisar jihar ta dawo da ƙarfinta.

    "Na ga yadda ɓangaren zartasta yake, yanzu abin da ake buƙata shi ne inganta ɓangaren majalisa. Kuma ba za su yi aiki cikin natsuwa ba, sai sun samu wurin aiki mai kyau," in ji Ibas, wanda ya samu rakiyar, shugaban ma'aikatan jihar, Dokta George Nwaeke.

  2. Girke-girken Ramadan: Yadda ake yin "Tortilla cone", wato burodi mai nama da kayan lambu

    A yau cikin filinmu na girke-girken Ramadan, Ahmad Hambali wanda aka fi sani da bn__hambal zai nuna muku yadda ake yin "Tortilla cone", wato wani nau'in burodi mara kauri wanda ake saka wa nama da kayan lambu cikinsa don ya yi kama da askirim.

    Bayanan bidiyo, Girke-girken Ramadan: Yadda ake yin "Tortilla cone", wato burodi mai nama da kayan lambu
  3. An gabatar da Magajin Garin Istanbul a kotu kan zargin cin hanci da taimakon ta'addanci

    Turkiya

    Asalin hoton, EPA

    Magajin Garin Istanbul na Turkiyya, Ekrem Imamoglu, ya bayyana a gaban kotu a ƙasar domin amsa tuhumarsa da ake yi da cin hanci da taimakon ƙungiyar ta'addanci.

    Tun da farko, lauyansa ya ce ba za su amince da tuhume-tuhumen ba, sannan ya ƙara da cewa Magajin Garin yana godiya tare da alfahari da waɗanda suka yi zanga-zanga domin nuna masa goyon baya, da kuma abin da ya bayyana da "ƙoƙarin kare martabar dimokuraɗiyyar ƙasar."

    Zanga-zangar dai ta faɗaɗa, wanda hakan ya sa hukumomi a ƙasar suka rufe hanyoyin sufuri da dama domin taƙaita ta.

    Sai dai duk da haka, masu zanga-zangar suna cigaba da tattakin, duk da kama ɗaruruwansu da aka yi.

    A gobe Lahadi ne ake sa ran babbar jam'iyyar adawa ta ƙasar, CHP za sanar da Mista Imamoglu a matsayin ɗantakararta na shugaban ƙasa.

  4. M23 za su fice daga birnin Walikale domin tattauna batun sulhu da gwamnatin Congo

    M23

    Asalin hoton, AFP

    Ƴantawayen M23 sun ce za su fice daga birnin Walikale da ke gabashin Dimokuraɗiyar Jamhuiyar Congo domin bayar da damar tattaunawa batun sulhu.

    Ƴantawayen, waɗanda suke samun goyon bayan Rwanda sun ƙwace iko ne da birnin a farkon wannan makon da muke ciki.

    Ƴan ƙungiyar suna ƙwace iko tare da mamaye birane da dama tun lokacin da suka fara gwabza yaƙi a watan Janairun bana.

    Walikale na cikin biranen da suka ƙwace, kuma birnin na can yamma mai nisa.

    Sai dai ba su bayyana inda mayaƙan za su koma ba har zuwa yanzu.

  5. Me tsarin mulki ya ce kan tsige gwamna a Najeriya?

    Rivers

    Asalin hoton, Martin Amaewhule/ Sir Siminalayi Fubara/ Facebook

    Tun bayan zaman tankiyar da ya ɓarke a jihar Rivers, wanda ya kai ga cewa shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ƙaƙaba dokar ta-ɓaci yan Najeriya ke ta neman sanin tanade-tanaden kundin tsarin mulkin ƙasar dangane da hanyoyi da kuma laifukan da ke janyo a tsige gwamna mai ci.

    Kafin ƙaƙaba dokar, ƴanmajalisar sun fara bin matakin farko na ƙoƙarin tsige gwamnan, ta hanyar aika masa da takarda ƙunshe da jerin laifukan da suke tuhumarsa da aikatawa.

    Ƙarin bayani - https://bbc.com.im/hausa/articles/c62zdnjpl99o%3C/a%3E%3C/p%3E%3C/div%3E%3C/div%3E%3C/article%3E%3C/li%3E%3Cli class="css-xxlek1">

    Dakatar da gwamnan Rivers ɓata sunan Najeriya ne a idon duniya — Jonathan

    Jonathan ya ce duk da cewar akwai buƙatar ɗaukar matakan da za su magance rikicin siyasar da ya dabaibaye jihar Rivers na tsawon lokaci, a cewarsa dakatar da waɗanda mutane suka zaɓa a matsayin shugabanninsu bai dace ba.

    Ya ƙara da cewa ya san bai kamata a matsayinsa tsohon shugaban ƙasa ya cika maganganu barkatai a game da abubuwan da suke a ƙasar ba, amma "yadda ake kallon Najeriya yana ta'allaƙa ne a kan matakan ɓangaren zartaswa da majalisa da na shari'a suka ɗauka," in ji shi.

  6. Me nasarar Najeriya a Rwanda ke nufi a neman zuwa gasar Kofin Duniya?

  7. Isra'ila ta kai munanan hare-hare a kudancin Lebanon

  8. Cutar mashaƙo ta sake kashe mutum a Najeriya

  9. Mai haƙa ƙabarin da 'aiki ke hana shi barci' saboda yaƙin Sudan

  10. Mutanen da hare-haren Isra'ila suka kashe a Gaza sun ƙaru, in ji ma'aikatar lafiya

    Falasɗinawa

    Asalin hoton, Reuters

    Hare-haren da sojojin Isra'ila ke cigaba da kaiwa kan Zirin Gaza tun daga ranar Talata sun kashe mutum 634, a cewar ma'aikatar lafiya ta zirin.

    Kazalika, hare-haren sun raunata wasu 1,172. Cikin mutanen, an kashe 130 cikin kwana biyu da suka wuce.

    Jimillar Falasɗinawa da aka kashe tun daga ranar 7 ga watan Oktoban 2023 yanzu sun kai 49,747 da kuma 113,213 da aka raunata, a cewar ma'aikatar.

  11. Jirage sun ci gaba da sauka a filin jirgi na Heathrow bayan dawowar lantarki

    Jiragen British Airways

    Asalin hoton, Reuters

    Jiragen sama sun ci gaba da zirga-zirga a filin jirgi na Heathrow da ke birnin Landan bayan dawo da lantarki.

    An rufe filin jirgin ne a ranar Juma'a, lamarin da ya haifar da ruɗu ga dubban matafiya bayan soke tashi da kuma saukar jirgi sama da 1,350.

    Hukumomin Heathrow sun ce suna fatan komai zai dawo daidai a filin jirgin a yau Assabar.

    Wakilin BBC ya ce an nuna shakku kan abin da zai faru nan gaba yayin da jirage da dama suka soke sauka da tashi lamarin da ya dagula lissafin matafiya.

  12. 'Yansandan Kaduna sun kama mutum 12 bayan kashe matashi a masallaci

    Kwamashinan 'Yansandan Kaduna

    Asalin hoton, Nigeria Police

    Rundunar 'yansadan Najeriya reshen jihar Kaduna ta ce ta kama mutum 12 da zargin kai hari masallaci a Kaduna da ke arewacin ƙasar.

    Wata sanarwa da kakakin rundunar a Kaduna, DSP Mansur Hassan, ya fitar ta ce harin ya yi sanadin kashe wani matashi mai suna Usman Mohammad mai shekara 23.

    A cewar DSP Mansur, rundunar 'yansandan ta samu rahoto daga wani mazaunin yankin Rigasa cewa 'yandaba ɗauke da makamai na shirin kai hari kan masu sallar Tahajjud.

    "Da jin rahoton ne kuma dakaru suka bazama amma kafin su ƙarasa har sun daɓa wa wani matashi mai suna Usman Mohammed wuƙa, wanda likita ya tabbatar da mutuwarsa a asibiti," in ji shi.

    Ya ce sun isa wurin ne bisa rakiyar dakarun sa-kai na Civilian Joint Task Force (CJTF), kuma tuni sun ƙaddamar da cikakken bincike kan lamarin.

  13. Gwamnatin Najeriya ta kama mutum 327 kan haƙar ma'adanai ta ɓarauniyar hanya

    Haƙar ma'adanai

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce ta kama mutum 327 da ake zargi da aikin haƙar ma'adanai ba bisa ƙa'ida ba a faɗin ƙasar.

    Ministan Ma'adanai Dele Alake ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a bikin cika shekara ɗaya da kafa rundunar kula da harkokin haƙar ma'adanai ta Mining Marshals (MM).

    Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ruwaito shi yana cewa an kama mutanen ne tun daga kafa rundunar a 2024 sun yi nasa, inda ma'aikatarsa ta yi nasarar gurfanar da 143 daga cikinsu a gaban kotu.

    Ya ƙara da cewa babban abin da suka saka a gaba a 2025 shi ne gurfanar da sauran mutanen a gaban shari'a.

    An ƙaddamar da rundunar MM ne ranar 21 ga watan Maris na 2024, inda ta fara aiki da dakaru 2,220 kafin su ƙaru zuwa 2,670, a cewar NAN.

  14. Isra'ila ta kai hare-hare ta sama a Syria

    Jirgin yaƙi

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta kaddamar da wasu hare-hare ta sama a wasu sansanoni biyu a Syria.

    Ta ce ta kai hare-haren ne a filin jirgin sama na soji da kuma wasu sansanonin sojin sama a Palmyra sakamakon bayanan sirri kan fataucin makamai.

    Kafofin yada labaran Syria sun ce an raunata jami'an tsaro biyu.

    Tun faduwar gwamnatin Bashar Al-Assad a watan Disamba, Isra'ila ke kai hare-hare a sansanonin sojin Syria, tana mai ikirarin tarwatsa makamai da take tsoron za su iya fadawa hannun mayakan da za su iya kai mata hari.

  15. Assalamu Alaikum

    Maraba da shigowa shafin labarai kai-tsaye na ranar Asabar.

    Umar Mikail ne zai kawo rahotonnin daga sassan duniya daga yanzu zuwa ƙarfe 4:00 na rana.

    Ku biyo mu.