Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya, Juma'a, 28/02/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sassan duniya kai tsaye, na Juma'a, 28/02/2025

Taƙaitattu

  • Tinubu ya sanya hannu kan kasafin kuɗin 2025
  • An ga watan Ramadan a Najeriya
  • An yi cacar baki tsakanin Donald Trump da Zelensky
  • An ga watan azumin Ramadan na 2025 a Saudiyya
  • Kotun Ƙoli ta amince da ɓangaren Wike na majalisar jihar Rivers

Rahoto kai-tsaye

Muhammad Annur Muhammad da Isiyaku Muhammed

  1. Aƙalla mutum shida sun mutu a wani harin ƙunar-baƙin-wake a Pakistan

    Aƙalla mutum shida ne suka mutu a wani harin ƙunar-baƙin-wake da aka kai masallacin wata makarantar Islamiyya a yankin arewa maso yammacin Pakistan inda aka san jagororin Taliban na karatu a can.

    Shugaban makarantar, Hamid ul Haq, na daga cikin waɗanda suka rasu a harin.

    Ba wata ƙungiya zuwa yanzu da ta fito ta ɗauki alhakin kai harin.

    Waɗanda suka ga harin sun gaya wa BBC, ɗaruruwan jama'a sun taru a babban a masallacin makarantar.

    An kai harin ne a masallacin Dar-ul-Uloom Haqqania bayan sallar Juma'a

    Shugaban Pakistan, Asif Ali Zardari, da Taliban sun yi Allah-wadari da harin.

  2. Ana fama da ɗaukewar wutar lantarki a Abuja har ma da fadar shugaban ƙasa

    Babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja ya gamu da matsalar ɗaukewar wutar lantarki sakamakon lalacewar wasu layikan da ke kai lantarkin sassan birnin na kamfanin da ke samar da wutar (AEDC) ya sanar.

    Hatta fadar gwamnatin ƙasar matsalar ɗaukewar wutar ta shafa kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito a yau Juma'a.

    Kamfanin samar da lantarkin (AEDC) a wata sanarwa da ya rinƙa fitarwa akai-akai a shafinsa na X, ya roƙi masu amfani da wutar da su yi haƙuri, yayin da ya ce ma'iakatansa na aiki tuƙuru domin shawo kan matsalar, don mayar da wutar ga sassan da abin ya shafa.

    To amma daman wasu unguwannin wajen birnin kamar su Lugbe da Kubwa daman sun yi kwanaki ba su da wutar lantarkin.

    A sanarwar da kamfanin ya fitar ya ambato unguwanni da yankuna da dama da matsalar ta shafa.

    A jiya Alhamis aka ruwaito ministan makamashi, Adebayo Adelabu, a lokacin gabatar da shiri da manufar gwamnatin ƙasar kan samar da lantarki ya nuna takaicinsa kan ci gaba da lalacewar kayan samar da lantarki a ƙasar.

    Ministan ya ɗora alhakin hakan a kan rashin aniyar kamfanonin rarraba lantarkin ta zuba jari a harkar.

  3. Yankunan Zamfara na kokawa da biyan ƴan bindiga kuɗin fansa

    Al'ummar garuruwan Zurmi da Shinkafi a jihar Zamfara na fuskantar matsin lamba wajen biyan ƴan bindiga kuɗin fansa, da ya kai fiye da naira miliyan ɗari uku.

    Yayin da wasu garuruwn kuma ke ci gaba da fuskantar hare-hare tare da kwashe masu kayan abinci, da dabobi.

    Hakan dai ya biyo bayan janyewar jami'an sojoji da ke yankin ne, a ranar Litinin da ta gabata.

    Bello Hassan Shinkafi shi ne ɗan majalisa mai wakiltar yankin na Zurmi da Shinkafi a majalsiar wakilan Najeriya, ya bayyana hakan a tattaunawarsa da BBC.

  4. Ana aikin ceto gomman ma'aikata da dusar ƙanƙara ta binne a India

    Masu aikin ceto a India na can suna neman kusan ma'aikatan gine-gine arba'in, waɗanda ake fargabatar dusar ƙanƙara ta binne a jihar Uttarakhand ta arewacin ƙasar.

    Zuwa yanzu an ceto mutum goma sa shida, amma kuma dusar ƙanƙarar mai yawa da ke zuba na haifar da matsala ga aikin ceton wasu gomman ma'aikatan.

    Matsalar zaftarewar dusar ƙanƙarar ta shafi yankin da ake aikin wani titi a gundumar Chamoli da ke kusa da iyakar ƙasar da Tibet.

  5. China ta zartar da hukuncin kisa a kan wata mata me safara da sayar da yara

    Hukumomin China sun aiwatar da hukuncin kisa a kan wata mata da kotu ta kama da laifin sacewa da kuma safarar yara 17 cikin shekara goma.

    Ana ganin yaro na farko da matar mai suna Yu Huaying ta yi safarar, ɗanta ne, wanda ta sayar a lokacin tana wajen shekara ashirin da wani abu.

    Matar mai shekara 61 ta aikata laifin ne a tsakanin 1993 zuwa 2003.

    Tana satar yara 'yan kimanin shekara biyar daga lardunan kudancin ƙasar ta sayar da su can a arewa.

    Lamarin ya tayar da hankali a ƙasar ta China wadda ta daɗe tana fama da matsalar safarar yara.

    "Yansandan ƙasar sun ce sun magance sama da matsaloli ɗari biyar na satar yaran a shekarar da ta wuce.

  6. Rundunar sojin Isra'ila ta gaza wajen kare farar hula a harin Hamas - Rahoto

    Rundunar sojin Isra'ila ta wallafa rahotonta na farko a kan kura-kuran da ta yi har Hamas ta kai harin 7 ga watan Oktoba, 2023, lamarin da ya haddasa yaƙin Gaza.

    Rahoton ya ayyana cewa rundunar sojin ta gaza a aikinta na kare farar hula.

    Rahoton mai shafi 19, yana ɗauke da wasu bayanai da tuni aka san su a kan abin da ya janyo harin na bazata.

    Harin ya janyo asarar rayuka kusan 1,200, lokacin da mayaƙan Hamas da sauran ƙungiyoyin Falasɗinawa suka far ma Isra'ilar har suka yi garkuwa da Isra'ilawa 251.

    Rahoton na ɗauke da bayanai kan yadda rundunar sojin ta gaza wajen sanin ƙarfi da dabarun Hamas.

  7. MDD da Kongo na neman tallafin dala biliyan biyu da rabi don taimaka wa jama'a

    Majalisar Ɗinkin Duniya da Jamhuriyar Dumukuraɗiyyar Kongo sun nemi tallafin dala biliyan biyu da rabi domin shawo kan matsalar jinƙai a Kongon, inda rikici ya shafi mutane kusan miliyan ashirin.

    Majalisar ta ce za a yi amfani da kuɗaɗen wajen taimaka wa mutanen da ke tsananin buƙata ciki har da mutum miliyan takwas da suka tsere daga muhallinsu.

    Ƴan tawayen M23 sun ƙwace wasu yankuna na ƙasar, lamarin da ya jefa mutane da dama cikin tsananin buƙatar agaji.

  8. Tattaunawar Isra'ila da Hamas kashi na biyu ta yi nisa a Masar

    Masar ta ce tattaunawa ta yi nisa tsakanin Isra'ila da Hamas kan kashi na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza a birnin Alƙahira.

    Isra'ila ta tura masu shiga tsakani bayan da aka yi musayar ɗaruruwan fursunoni Falasdinawaa da 'yan Isra'ila.

    Aƙalla ƴan Isra'ila sittin ne ke Gaza, inda hukumomin Isra'ilar suka yi amanna cewa 24 kadai ke raye.

    A kashi na biyu na yarjejeniyar za a saki dukkan ƴan Isra'ila tare da kawo ƙarshen yaƙi baki ɗaya.

  9. Mexico ta aika madugun safarar miyagun ƙwayoyi da mutum 28 Amurka

    Ƙasar Mexico ta tasa ƙeyar wasu mutane 29 da ake zargin ‘yan ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ne zuwa Amurka, ciki har da manyan shugabannin ƙungiyoyin.

    Ana kallon matakin a matsayin wani babban yunƙuri na inganta dangantakar tsaro tsakanin ƙasashen biyu.

    Shugaba Trump ya yi barazanar ƙaƙaba wa Mexico haraji, inda ya zargi ƙasar da gazawa wajen shawo kan matsalar kwararar ƙawaya da ƴancirani.

    Wakilin BBC ya ce yana tunanin hakan wani yunƙuri ne da gwamnatin Mexico ta yi na bayar da hadin kai kan tsaron kan iyakoki da kwararar baƙin haure zuwa Amurka.

  10. Tsofaffin sakatarorin tsaron Amurka sun soki shirin Trump na korar ma'aikatan tsaro

    Tsofaffin sakatarorin tsaron Amurka biyar sun rubuta wasiƙa ga majalisar dokokin ƙasar inda suka yi Allah-wadarai da korar manyan jami’an ma'aikatar tsaro, inda suka kira matakin da rashin tunani.

    Sun ɗauki matakin ne kwana ɗaya bayan da Shugaba Trump ya ƙaddamar da shirin korar manyan jami'an tsaron ƙasar tare da aniyar korar ma'aikata da dama a ƙasar.

    A cikin wasiƙar, sakatarorin tsaron da suka yi aiki ƙarƙashin gwamnatin dukkan manyan jam'iyyun Amurka sun ce hakan wata alama ce da ke nuna alamar siyasantar da ɓangaren tsaron ƙasar.

  11. Shugaba Trump da Firaministan Birtaniya sun gana kan Ukraine

    Firaiministan Birtaniya Keir Starmer da Shugaba Trump sun gana a fadar white House kan yaƙin Ukraine.

    Trump ya ce shirye-shirye sun yi nisa wajen kawo ƙarshen hare-haren Rasha, sai dai bai bayar da tabbacin samar da tsaro ga Ukraine ba.

    Mista Starmer wanda a baya ya yi alƙawarin tura dakarun Birtaniya Ukraine ya ce suna neman goyon bayan Amurka.

    Wakiliyar BBC ta ce Trump ya ce dole ne sai an samar da yarjejeniya za a iya duba wasu batutuwan.

    Shi kuwa shugaba Zelensky ya isa Amurka a yau Juma'a domin rattaba hannu kan yarjejeniyar haƙo ma'adanai a Ukraine.

  12. Buɗewa

    Masu bibiyarmu a wannan shafin da ke kawo muku labaran abubuwan da ke wakana a Najeriya da sauran sassan duniya kai tsaye, muna muku maraba a wannan safiya ta Juma'a, 28/02/2025.

    Za mu kasance da ku daga yanzu zuwa wani lokaci a nan gaba.

    Za kuma ku iya leƙawa shafukanmu da sada zumunta domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo, har ma ku yi muhawara.

    Mu fara da wannan karin maganar - Komai daɗewar gungume a ruwa ba zai zama kada ba