KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 27/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Asabar 27 ga watan Yunin 2026.

Taƙaitattu

Skip Bidiyo and continue reading
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. NDLEA ta ƙwace miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta kai naira biliyan 5 a Rivers

    ....

    Asalin hoton, NDLEA/x

    Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeirya (NDLEA) ta ce ta ƙwace miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta kai kusan Naira biliyan 5 a tashar jiragen ruwan Onne da ke jihar Rivers.

    Kwamandan NDLEA a tashar, Omerio Odo, ne ya bayyana hakan yayin bikin ranar yaƙi da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ta duniya a 2026.

    Ya ce kayayyakin da aka kama sun haɗa da kwantena guda bakwai ɗauke da sama da kwayoyi miliyan 3.5 na opioids da kuma kwalabe miliyan 1.2 na codeine, tare da kayan da nauyinsu suka kai ton 206.

    Ya ƙara da cewa an samu wannan nasara ne ta hanyar tattara bayanan sirri, ƙara tsauraran matakan sa ido da kuma haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki a harkokin jiragen ruwa.

    Odo ya bayyana cewa kayayyakin da aka kama kaya ne da za su shafi rayuwar mutane da iyalai da kuma al’umma baki ɗaya. Ya kuma yi gargaɗin cewa duk da muhimmancin tashar Onne wajen kasuwanci, masu safarar miyagun ƙwayoyi na ƙoƙarin amfani da hanyoyin ruwa wajen shigo da haramtattun kaya cikin ƙasar.

    Kwamandan ya tabbatar da cewa NDLEA za ta ci gaba da ƙara ƙaimin matakai ba ƙaƙƙautawa wajen daƙile fataucin miyagun ƙwayoyi, tare da jaddada buƙatar haɗin kai daga gwamnati, al’umma da hukumomi.

    Ya kuma bukaci masu harkokin dakon kaya da su riƙa bincika kayayyaki sosai tare da bayar da rahoton duk wani abu da ake zargi.

  2. An gurfanar da ƙarin mutum 17 kan kisan matar da aka ƙona a Kaduna

    ....

    Asalin hoton, Family

    Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta sanar da gurfanar da wasu ƙarin mutane 17 da ake zargi da hannu a kisan gayyan da aka yi wa wata mata a Ungwar maraban Jos, na jihar Kaduna a makon da ya gabata.

    Wata sanarwar da ta fito daga ofishin jami'in hulɗa da jama'a na rundunar DSP Mansir Hassan ta ce an gurfanar da waɗanda ake zargin ne yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.

    Sabarwar ta ƙara da cewa bayan kammala binciken farko, an gurfanar da wasu mutane talatin da uku (33) da ake zargi da laifin haɗa baki da kuma yin taro ba bisa ƙa’ida ba.

    Rundunar ta kuma bayyana cewa mutane talatin (30) da aka kama bayan aukuwar lamarin, ba same su da hannu wajen aikata laifin ba, kuma an sake su ba tare da wani sharaɗi ba.

    Rundunar ta sake nanata cewa ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin, inda ta bayar da tabbacin cewa ta na ƙara ƙaimi wajen ganowa da kamo duk waɗanda ke da hannu, ko kuma suka taimaka wajen aikata wannan laifi.

  3. Iran ta zargi Amurka da ƙeta yarjejeniya bayan hare-haren soji

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana hare-haren da Amurka ta kai a matsayin “karya yarjejeniya a fili,” tana mai cewa hakan ya ci karo da yarjejeniyar da aka ƙulla tsakanin ƙasashen biyu domin kawo karshen yaki.

    A cikin wata sanarwa, ma’aikatar ta ce harin da Amurka ta kai a gaɓar tekun Iran” ya saɓawa Mataki na 2, Sashe na 4 na Yarjejeniyar Majalisar Ɗinkin Duniya, tare da ƙeta Sashe na 1 na Yarjejeniyar fahimtar juna kan kawo karshen yaki da aka sanyawa hannu a ranar 18 ga Yuni..

    Haka kuma, Iran ta bayyana harin da Isra’ila ta kai a Lebanon a matsayin “keta yarjejeniya” tana mai ɗora alhakin sakamakon abubuwan da ke faruwa kan Amurka da sauran ɓangarorin da ta ce suna da hannu wajen goyon bayan matakan da Amurka ke ɗauka kan Iran.

    A daren jiya, rundunar sojin Amurka (CENTCOM) ta sanar da cewa jiragen yaƙinta sun kai hari kan rumbunan makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa na Iran, da gabar teku.

    Bayan waɗannan hare-hare, Rundunar IRGC ta Iran ta ce ta mayar da martani ta hanyar kai hari kan wuraren da sojojin Amurka ke jibge a yankin.

  4. Adadin mutanen da suka mutu a girgizar ƙasar Venezuela ya haura 900

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Mahukunta a Venezuela sun ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon girgizar ƙasa biyu masu ƙarfi da suka afku a ranar Laraba ya haura mutum 900, yayin da Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce sama da mutane 50,000 har yanzu ana nemansu ba a same su ba.

    A yammacin ranar Juma’a kuma, an ji wata sabuwar girgizar ƙasa mai matsakaicin ƙarfi a tekun arewacin Venezuela.

    Cibiyar Nazarin Girgizar Ƙasa ta Euro-Mediterranean (EMSC) ta ce karfin girgizar ya kai maki 4.9.

    Shaidu sun ce an ji girgizar a babban birnin ƙasar, Caracas, da kuma birnin Maracay da ke arewa.

    Dubban mutane na ci gaba da karɓar magani sakamakon raunukan da suka samu daga girgizar ranar Laraba, inda da dama daga cikinsu ke kwance a asibitocin wucin-gadi.

    Gine-gine da dama a arewacin Venezuela, ciki har da Caracas, sun lalace ko kuma sun rushe sakamakon waɗannan girgizar ƙasa, lamarin da ya ƙara tsananta halin da ake ciki yayin da ake ci gaba da aikin ceto waɗanda suka maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzai.

  5. Jami’an Iran sun soki sanarwar ƙasashen Gulf kan goyon bayan Amurka

    Jami’an Iran sun ci gaba da mayar da martani mai tsauri ga sanarwar da Ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Gulf (GCC) ta fitar wadda ta nuna damuwa kan matakan Iran a yankin tare da jaddada goyon baya ga tsaron ƙasashen Gulf da kuma alaƙa da Amurka.

    Shugaban Kwamitin Tsaro na Majalisar Dokokin Iran, Ebrahim Azizi, na daga cikin jami’an da suka mayar da martani, inda ya gargaɗi ƙasashen membobin ƙungiyar da cewa, “yin fare da tsarin Amurka zai lalata tsaro da kwanciyar hankalinku.”

    Da yake ishara da hare-haren da Iran ta kai kan wasu ƙasashen yankin Tekun Fasha yayin rikicin da ya shafi Amurka da Isra’ila, Azizi ya ce: “Kun ga yadda sansanonin sojin Amurka da ke ƙasashenk ya zamo tushen barazana maimakon samar da tsaro.”

    Azizi ya kuma bayyana cewa “ƙarfin makamai masu linzami da jiragen yaki marasa matuƙa da kuma kula da mashigar ruwan Hormuz,” su ne manyan lamarin da Iran da ba za ta bari a ƙetare ba.

    Duk da cewa Iran ba ta tabbatar ko ƙaryata harin da aka kai kan wani jirgin dakon kaya a jiya ba, Azizi ya jaddada cewa, “hanya ɗaya tilo da za a tabbatar da tsaron yankin ita ce nesanta kai da Amurka.”

    Kalaman shugaban kwamitin tsaron majalisar sun biyo bayan martanin wasu jami’an Iran da dama kan sanarwar da ƙasashen GCC suka fitar.

    .

  6. Mun kai hari kan sansanonin sojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya - Iran

    ...

    Asalin hoton, IRNA

    Rundunar juyin juya halin Iran (IRGC) ta bayyana cewa rundunar ruwanta ta kai hari kan wasu wuraren da sojojin Amurka ke jibge a yankin Gabas ta Tsakiya, a matsayin martani ga hare-haren da Amurka ta kai a gaɓar tekun Iran.

    A wata sanarwa da sashen hulɗa da jama’a na IRGC ya fitar, ta ce Amurka ta kai hare-haren sama kan gaɓar tekun Iran bayan ta kai farmaki kan wani jirgi a mashigar ruwan Hormuz, bisa hujjar cewa jirgin yana bi ta wata hanya da Iran ke ganin “ba ta da izini.”

    IRGC ta bayyana hare-haren a matsayin ƙeta yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma alƙawuran da Amurka ta ɗauka.

    Sai dai sanarwar ba ta yi ƙarin bayani kan inda aka kai hare-haren ba, ko irin makaman da aka yi amfani da su, da kuma irin ɓarnar da aka yi.

    Haka kuma, sanarwar ta ce bisa ga Mataki na 5 na Yarjejeniyar Islamabad, kula da zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar Hormuz na karkashin alhakin Iran ne.

    IRGC ta gargaɗi Amurka cewa idan aka sake kai hare-hare, Iran za ta mayar da martani mafi tsanani.

  7. Assalamu alaikum!

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,Barkanmu da Safiyr ranar Asabar.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.