Za mu kai hari kan dakarun Amurka idan suka bi ta Mashigar Hormuz - Iran
Rundunar sojin Iran ta ce za ta kai hari kan dakarun Amurka idan har suka shiga Mashigar Hormuz - bayan da shugaba Trump ya ce Rundunar sojin Amurka za ta fara raka jiragen ruwan ƴan kasuwa da za su wuce ta Mashigar Hormuz, a yau litinin
Sanarwar ta ce shirin, wanda Mista Trump ya yi wa laƙabi da Project Freedom, zai kunshi dakarun sojin Amurka dubu goma sha biyar, da jiragen ruwan yaƙi masu lalata makamai masu linzami da kuma jiragen saman yaƙi sama da ɗari.
Wakilin BBC ya ce shugaban ya ce Amurka za ta raka waɗannan jiragen ruwan su fice daga yankin, kuma za zu ci gaba da gudanar da kasuwancinsu ba tare da wata matsala ba.
Tun da farko dai, Wani babban jami'in Iran Ebrahim Azizihas ya yi gargadin cewa za a ɗauki duk wani yunƙurin Amurka na yin katsalandan a harkokin mashigar ruwan a matsayin keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma.