Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 30/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Juma'a 30 ga watan Janairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammed, Aisha Babangida da Ahmad Bawage

  1. Za mu mayar da martani idan aka kai mana hari - Iran

    Shugaba Trump ya ce yana son kauce wa ƙaddamar da harin soja a kan Iran, ko da yake al'amura na iya sauyawa idan har Tehran din ta ci gaba da shirinta na Nukiliya.

    Ya shaida wa 'yan jarida a birnin Washington cewa zai yi magana da Iran din. Tehran dai ta yi barazanar duk wanda ya ce kule, za ta ce masa cas.

    Wani babban jami'in sojan kasar Birgediya Janar Mohammad Akraminia, ya ce karfin sojinsu, ta kai su iya kai hari kan duk wani sansanin sojin Amurkar da ke gabas ta tsakiya.

    Da farko Shugaba Trump ya yi gargaɗin cewa sojojin Amurkar za su kai hari idan Tehran ta kashe fararen hula da ke zanga-zangar adawa da gwamnati ne, kafin daga bisani ya sauya tunani.

  2. Buɗewa

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Juma'a daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.