Amurka ta dakatar da shigar ƴan Afghanistan ƙasar bayan an harbi wasu jami'an tsaro
Maaikatar harkokin wajen Amurka ta ce ta dakatar da duba buƙatar duk wasu takardu na ƴan Afghanistan na shiga ƙasar har sai abin da hali ya yi, bayan da aka harbi wasu jamian tsaro na tarayya biyu a Washington.
Shugaba Trump ya ce mutumin da ake zargi da kai harin ɗan Afghanistan ne da ya shiga kasar a 2021.
An bai wa Dubban ƴan Afghanistan da suka yi aiki da Amurka wata kariya ta musamman ta zama a Amurka bayan da Amurka ta janye daga ƙasarsu kuma suka faɗa yanayi na ramuwar gayya daga Taliban.