Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 27/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Juma'a 27 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza

  1. Yadda dajin Kainji ke neman zama maɓoyar ƙungiyoyin ƴanbindiga a Najeriya

    A farkon watan Fabrairun shekarar 2026 ne mahara sama da 100 suka yi dirar mikiya sanye da kayan sojoji a ƙauyukan Woro da Nuku da ke jihar Kwara da ke arewa ta tsakiya a Najeriya, inda suka kashe sama da mutum 75.

    Sun dira a ƙauyukan ne da yammacin ranar Talata a daidai lokacin da manoman ƙauyukan suke komawa gida daga gonakinsu.

    Babban abin da ya ja hankali shi ne yadda maharan suka aika da wasiƙar zuwa garin domin "wa'azi", sannan suka shiga, suka yi aika-aikarsu, sannan suke fice ba tare da fuskantar matsala ba.

    Bayan harin ne gwamnatin Najeriya ta zargi mayaƙan Boko Haram da kai harin, duk da cewa ƙungiyar ba ta ɗauki alhaki ba, duk da cewa ta fi gudanar da ayyukanta a arewa maso gabashin Najeriya.

    A lokacin ne mutane suka fara tambayar wai daga ina maharan suka taso, kuma su wane ne su?

  2. Jam'iyyun adawa sun yi watsi da sabuwar dokar zaɓe

    Jagororin manyan jam’iyyun adawa a Najeriya sun yi watsi da sabuwar dokar zaɓe ta 2026 da aka yi wa gyara wadda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanya wa hannu kwanan nan.

    Sun buƙaci majalisar Najeriya ta gaggauta fara sabon tsarin gyara dokar, suna zargin jam’iyyar APC da shirin amfani da gyaran wajen yin magudi a zaɓen 2027.

    Tinubu ya rattaɓa hannu kan dokar ne bayan majalisar dokoki ta yi mata gyara, amma tun kafin hakan ake ta ce-ce-ku-ce da zanga-zanga daga ɓangaren adawa da ƙungiyoyin farar hula.

    Waɗannan ɓangarori sun dage cewa wajibi ne a riƙa tura sakamakon zaɓe kai tsaye ta na’ura maimakon tanadin amfani da tsarin takarda da ’yan majalisa suka saka.

    A wata sanarwa bayan wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis, tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya ce "shi da sauran shugabannin adawa ba su amince da sabuwar dokar ba saboda an gaggauta amincewa da ita ba tare da la’akari da muradun jama’a ba.:

    Ya kuma nuna goyon baya ga shugaban jam’iyyar NNPP, Dr Ajuji Ahmed, wanda ya soki sashe na 60(3) da ke bai wa hukumar INEC damar amfani da tsarin takarda maimakon nuna sakamakon zabe kai tsaye ta na’ura idan aka ce an samu tangardar na'ura.

    A cewarsu, sabuwar dokar ta sabawa dimokuraɗiyya kuma yunƙuri ne na rage gaskiya da sahihancin zaɓe..

  3. Inec ta sauya ranar zaɓen shugaban Najeriya na 2027

    Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya (INEC) ta sanya sabbin ranakun gudanar da zaben shugaban kasa da gwamnoni da kuma na ’yan majalisun tarayya da na jihohi na kasar na 2027.

    Hakan na zuwa ne mako biyu bayan hukumar ta fitar da jadawalin zaben na farko, wanda ya sha suka daga bangarori da dama kasancewar ranakun da hukumar ta sanar za su iya fadawa cikin watan azumin Ramadana na shekarar 2027.

    Lamarin ya kai ga cewa majalisar dokokin kasar ta yi gyara ga dokar zaben kasar game da lokaci mafi kankanta na sanar da ranar gudanar da zabe.

    A jadawalin farko da hukumar ta fitar, ta sanya ranar 20 ga watan Fabarairun 2027 a matsayin ranar zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin tarayya, sai kuma 6 ga watan Maris 2027 a matsayin ranar zaben gwamnonin jihohi da na ‘yan majalisar dokokin jihohi.

    Sa dai a cikin sanarwar da hukumar ta fitar ranar Alhamis, 26 ga watan Fabarairun 2025, wadda ta samu sa hannun shugaban kwamitin wayar da kan masu kada kuri’a Mohammed Kudu Haruna, ta ce: “bayan yin gyara ga dokar zabe ta 2022, da kuma amincewa da dokar zabe ta 2026, hukumar ta yi gyara tare da sauye-sauye ga lokutan shirye-shiryen zabe da kuma na zabukan domin ya yi daidai da tsarin sabuwar doka”.

  4. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Juma'a da ake kira da juma'atu babban rana.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.