Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ƙaryata raɗe-raɗin da ake yaɗawa cewa ya yanke jiki ya faɗi, har an fitar da shi asibiti a ƙasar waje, inda ya ce labari ne ƙirƙirarre.
Wike ya bayyana haka ne a Abuja a ranar Alhamis a lokacin da ya je ziyarar duba wani aiki wanda za a ƙaddamar a watan gobe domin bikin cikar Shugaba Bola Tinubu shekara biyu a mulki.
A wata sanarwa da daraktan yaɗa labaransa, Anthony Ogunleye ya fitar, Wike ya ce maƙiyansa na siyasa ne suka ƙirƙiri maganar domin su kawar da hankalin mutane.
"Abin da yake faruwa shi ne saboda tsohon shugaban ma'aikatan jihar Rivers ya fito ya bayyana gaskiyar abin da ya faru na yunƙurin saka bam a majalisar dokokin jihar da ma yunƙurin kai hari a kan kadarorin gwamnati, shi ne domin su kawar da hankalin mutane daga maganar, sai suka ƙirƙiri wannan labarin. Babu inda na yanke jiki na faɗi ballantana ma a garzaya da ni ƙasar waje."
Wike ya ce ko ranar da Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi buɗa-baki kan zagayowar haihuwarsa ya je, "ranar Sallah kuma na jagoranci mazauna Abuja domin zuwa taya shugaban ƙasar barka da sallah. Amma irin maganganun na siyasa ba sa damuna, kuma ba za su kawar mana da hankalinmu ba," in ji shi.