Gidan talbijin ɗin ƙasar Iran, Nour News ya ce aƙalla mutum 78 ne suka mutu sannan ƙarin 329 ne suka jikkata sakamakon hare-haren Isra'ila a wasu yankunan birnin Tehran da dare.
Sai dai kuma kafar a shafinta na Telegram ta ce alƙaluman ba na hukuma ba ne.
"Ba mu tantance waɗannan alƙaluma ba. Za mu kawo muku ƙarin bayani da zarar mun samu."
A wani ɓangare kuma rundunar sojin Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare kan Iran - inda ta ƙara harar babbar cibiyar ayyukan inganta sinadarin Uranium din Iran din da ke Natanz, tare kuma da lalata filin jirgin saman Tabriz.
Wakilin BBC ya ce manyan hare-haren na Israila na nuna manufa uku - lalata shirin nukiliya na Iran da kassara karfinta na kariya da kuma kashe masana kimiyyarta.
Tun da farko Isra'ilar ta hallaka shugabannin sojojin Iran da dama, inda ta kashe shugabannin rundunonin sojin kasar, da kuma babban jagoron sojojin juyin-juya-hali, da sauran manyan kwamandoji.
Isra'ila ta kai hare-haren a akalla birane shida, ciki har da yankunan da jama'a ke zaune a babban birnin ƙasar Tehran.
Iran ta mayar da martani da harba sama da jirage marassa matuka dari daya a kan Israila.
Israila wadda ke rufe ofisosin jakadancinta - na dan wani lokaci - a ƙasashen duniya ta ce ta kai harin ne domin tabbatar da wanzuwarta.