Rediyo da talabijin na Nijar sun koma aiki bayan katsewa na dan lokaci

Asalin hoton, Getty Images
Mazauna birnin Niamey sun shaida wa BBC cewa gidajen rediyo da talabijin na gwamnatin Nijar sun koma bakin aiki bayan katsewar dan lokaci.
Rahotanni sun ce kafafen sun koma aiki da misalin karfe 10:30 na safe agogon ƙasar, bayan sun katse shirye-shiryensu da misalin karfe 9:00 na safe.
Katsewar ta zo ne a daidai lokacin da aka ruwaito karar harbe-harbe da fashe-fashe a wasu sassan Niamey, ciki har da yankin filin jirgin sama na Diori Hamani, wani sansanin soja da kuma kusa da fadar shugaban ƙasa.
Mahukuntan Nijar sun yi kira ga jama'a da su kwantar da hankulansu, amma har yanzu ba su yi karin bayani kan abin da ya faru ba.





















