Mahara sun harbe mutum huɗu a masallaci yayin taron Ashura
Ƴansanda a ƙasar Oman sun ce aƙalla mutum hudu ne aka kashe tare da jikkata wasu da dama a harin da aka kai masallacin Wadi al-Kabir da ke kusa da babban birnin ƙasar Muscat.
Hotunan da aka yaɗa a intenet sun nuna yadda mutane ke ƙoƙarin tserewa daga masallacin da aka bude wa wuta.
Rahotonni sun ce mutanen sun taru a masallacin ne domin yin taron Ashura, wanda mabiya Shi'a ke yi duk shekara.
Ba a cika samun irin wannan rikici a Oman ba.
A gefe guda kuma, Ofishin Jakadancin Amurka ya yi kira ga ƴan ƙasarsa su yi taka tsantsan.