Ƙasashen Musulmi 8 sun yi alawadai da shirin Isra’ila na gina matsuguni a Yammacin Kogin Jordan
Ƙasashen Musulmi guda takwas sun fitar da sanarwar haɗin gwiwa inda suka yi Allah-wadai da manufofin Isra’ila na gina matsugunan Yahudawa a Yammacin Kogin Jordan.
Ministocin harkokin wajen ƙasashen da suka haɗa da Pakistan, Masar, Indonesia da Saudiyya sun yi watsi da shirin gina sabon babban matsugunin E-1, suna cewa hakan na iya ƙara rura wutar rikici.
Shirin gina matsugunin ya kuma fuskanci suka daga wasu ƙasashe saboda muhimmancin yankin da ake son gina shi, wanda ke tsakanin gabashin birnin Kudus da sauran sassan Yammacin Kogin Jordan.